< Torati 19 >

1 Wakati Yahwe Mungu wenu anayafutilia mbali mataifa, yale ambayo Yahwe Mungu wenu anawapa nchi yao, na wakati mnakuja kwao na kuishi katika miji yao na nyumba,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
2 mnapaswa kuchagua miji mitatu kwa ajili yenu katikati mwa nchi yenu ambayo Yahwe Mungu anawapa kuimiliki.
sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
3 Mnapaswa kujenga barabara na kugawa mipaka ya nchi yenu katika maeneo matatu, nchi ambayo Yahwe Mungu wenu anafanya kuimiliki, ili kwamba kila mmoja anayeua mtu mwingine apate kukimbia hapo.
Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
4 Hii ni sheria kwa ajili ya mtu anayeua mwingine na anayekimbilia huko kuishi: yeyote auae jirani yake bila kujua, na hapo awali hakumchukia-
Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
5 kama wakati mtu aingiapo katika msitu pamoja na jirani yake kukata kuni, na mkono wake ukata mti chini kwa shoka, na kichwa uteleza kutoka kwenye mpini na kumpiga jirani yake mpaka akafa- basi mtu huyu anapaswa kukimbilia katika moja ya miji hii na kuishi.
Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
6 Vinginevyo damu ya mlipiza kisasi atamfuata yeye aliyetoa uhai, na kwa hasira kali anampita kwa sababu ilikuwa safari ndefu. Na anampiga na kumuua, ijapokuwa mtu huyo akustahili kufa; na hata akustahili adhabu ya kifo kwa sababu hakumchukia jirani yake kabla hili halijatokea.
In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
7 Basi sasa ninakuamuru kuchagua miji mitatu kwa ajili yako.
Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
8 Kama Yahwe Mungu wenu apanua mipaka yenu, kama alivyoapa kwa mababu zenu kufanya, na kuwapa nchi yote ambayo amewaahadia kuwapa mababu zenu;
In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
9 kama mnazishika amri hizi zote kuzifanya, ambazo ninakuamuru leo- amri za kumpenda Yahwe Mungu wenu na daima kutembea katika njia zake, basi mnapaswa kuongeza miji mitatu zaidi kwa ajili yenu, isipokuwa ile mitatu.
idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
10 Fanya hivi ili kwamba damu isiyo na hatia isimwangwe katikati ya nchi ambayo Yahwe Mungu wenu anawapa kwa ajili ya urithi, ili kwamba pasiwepo hatia ya damu kwenu.
Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
11 Lakini kama yeyote anamchukia jirani yake, uongo unamsubiri, uinuka dhidi yake, na majeraha ya kufa kwake ili kwamba anakufa, na kama basi anakimbia katika moja ya miji hii-
Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
12 basi wazee wa mji wake wanapaswa kumtoa na kumrudisha toka huko, na kumkabizi katika mkono wa ndugu mhusika, ili kwamba amuue.
dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
13 Jicho lako halipaswi kumuonea huruma; badala yake; unapaswa kuondoa hatia ya damu kutoka Israel, ili kwamba iwe vizuri kwako.
Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
14 Haupaswi kuondoa alama ya jirani yako ambayo wameweka katika eneo muda mrefu, katika urithi wako ambao utarithi, katika nchi ambayo Yahwe Mungu wako anakupa kumiliki.
Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
15 Shahidi moja peke hapaswi kuinuka dhidi ya mtu kwa ajili ya uovu wowote, au kwa ajili ya dhambi yoyote, katika jambo lolote ambalo amefanya dhambi; kwa kinywa cha mashahidi wawili, au kwa kinywa cha mashahidi watatu, kunapaswa jambo lolote lilithibitishwe.
Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
16 Kama ushuhuda wa mtu asiye na haki anainua dhidi ya mtu yeyote kushuhudia dhidi yake kwa mambo mabaya.
In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
17 Basi watu wote wawili, mmoja kati ya yule utata upo, anapaswa kusimama mbele ya Yahwe, mbele ya makuhani na waamuzi ambao wanatumika siku hizo.
dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
18 Waamuzi wanapaswa kuchunguza kwa uangalifu; ona, kama ushahidi ni ushahidi wa uongo na umeshuhudiwa kwa uongo dhidi ya ndugu yake,
Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
19 basi unapaswa kufanya kwake, kama alivyokusudia kufanya kwa ndugu yake, na utaondoa uovu kutoka miongoni mwenu.
to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
20 Basi wale wanaobaki watasikia na kuogopa, na kuanzia hapo na kuendelea hawatafanya tena aina ya ouvu miongoni mwao.
Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
21 Macho yako hapaswi kuona huruma; maisha yatalipa kwa maisha, jicho kwa jicho, jino kwa jino, mkono kwa mkono, mguu kwa mguu.
Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.

< Torati 19 >