< Zaburi 94 >

1 Ee Bwana, ulipizaye kisasi, Ee Mungu ulipizaye kisasi, uangaze sasa.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Ee Mhukumu wa dunia, inuka, uwalipize wenye kiburi kama wanavyostahili.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Hata lini, waovu, Ee Bwana, hata lini waovu watashangilia?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 Wanamimina maneno ya kiburi, watenda mabaya wote wamejaa majivuno.
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Ee Bwana, wanawaponda watu wako, wanawaonea urithi wako.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Wanamchinja mjane na mgeni, na kuwaua yatima.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Nao husema, “Bwana haoni, Mungu wa Yakobo hafahamu.”
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Sikizeni, enyi wajinga miongoni mwa watu; enyi wapumbavu, lini mtakuwa na hekima?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Je, aliyeweka sikio asisikie? Aliyeumba jicho asione?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Je, anayeadhibisha mataifa asiadhibu? Je, awafundishaye wanadamu asiwe na maarifa?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 Bwana anajua mawazo ya mwanadamu; anajua kwamba ni ubatili.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Ee Bwana, heri mtu anayeadhibishwa na wewe, mtu unayemfundisha kwa sheria yako,
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 unampa utulivu siku za shida, mpaka shimo litakapokuwa limechimbwa kwa ajili ya mwovu.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Kwa kuwa Bwana hatawakataa watu wake, hatauacha urithi wake.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Hukumu itasimamishwa tena kwenye haki, wote walio na mioyo minyofu wataifuata.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Ni nani atakayeinuka dhidi ya mwovu kwa ajili yangu? Ni nani atakayenikinga dhidi ya watenda maovu?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Kama Bwana asingelinisaidia upesi, ningelikuwa ninaishi katika ukimya wa kifo.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Niliposema, “Mguu wangu unateleza,” Ee Bwana, upendo wako ulinishikilia.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Wakati wasiwasi ulipokuwa mwingi ndani yangu, faraja yako ilinipa furaha nafsini mwangu.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Je, kiti cha utawala wa udhalimu kitajiunga nawe, ule utawala uletao taabu kutokana na sheria zake?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Huungana kuwashambulia wenye haki, kuwahukumu kufa wasio na hatia.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Lakini Bwana amekuwa ngome yangu, na Mungu wangu amekuwa mwamba ninaoukimbilia.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 Yeye atawalipa kwa ajili ya dhambi zao na atawaangamiza kwa ajili ya maovu yao; Bwana Mungu wetu atawaangamiza.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Zaburi 94 >