< Zaburi 66 >

1 Kwa mwimbishaji. Wimbo. Zaburi. Mpigieni Mungu kelele za shangwe, dunia yote!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Imbeni utukufu wa jina lake; mpeni sifa zake kwa utukufu!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Mwambieni Mungu, “Jinsi gani yalivyo ya kutisha matendo yako! Uwezo wako ni mkuu mno kiasi kwamba adui wananyenyekea mbele zako.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Dunia yote yakusujudia, wanakuimbia wewe sifa, wanaliimbia sifa jina lako.”
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Njooni mwone yale Mungu aliyoyatenda, mambo ya kutisha aliyoyatenda miongoni mwa wanadamu!
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Alifanya bahari kuwa nchi kavu, wakapita kati ya maji kwa miguu, njooni, tumshangilie.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Yeye hutawala kwa uwezo wake milele, macho yake huangalia mataifa yote: waasi wasithubutu kujiinua dhidi yake.
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Enyi mataifa, msifuni Mungu wetu, sauti ya sifa yake isikike,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 ameyahifadhi maisha yetu na kuizuia miguu yetu kuteleza.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Ee Mungu, wewe ulitujaribu, ukatusafisha kama fedha.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Umetuingiza kwenye nyavu na umetubebesha mizigo mizito migongoni mwetu.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Uliwaruhusu watu watukalie vichwani, tulipita kwenye moto na kwenye maji, lakini ulituleta kwenye nchi iliyojaa utajiri tele.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Nitakuja hekaluni mwako na sadaka za kuteketezwa na kukutimizia nadhiri zangu:
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 nadhiri ambazo midomo yangu iliahidi na nilizotamka kwa kinywa changu nilipokuwa katika shida.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Nitakutolea dhabihu za wanyama wanono na sadaka za kondoo dume, nitakutolea mafahali na mbuzi.
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Njooni msikilize ninyi nyote mnaomcha Mungu, nami niwaambie aliyonitendea.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Nilimlilia kwa kinywa changu, sifa zake zilikuwa katika ulimi wangu.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Kama ningekuwa nimeyaficha maovu moyoni mwangu, Bwana asingekuwa amenisikiliza;
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 lakini hakika Mungu amenisikiliza na amesikia sauti yangu katika maombi.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Sifa apewe Mungu, ambaye hakulikataa ombi langu wala kunizuilia upendo wake!
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Zaburi 66 >