< Zaburi 61 >

1 Kwa mwimbishaji. Kwa ala za nyuzi za uimbaji. Zaburi ya Daudi. Ee Mungu, sikia kilio changu, usikilize maombi yangu.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2 Kutoka miisho ya dunia ninakuita, ninaita huku moyo wangu unadhoofika; uniongoze kwenye mwamba ule ulio juu kuliko mimi.
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3 Kwa kuwa umekuwa kimbilio langu, ngome imara dhidi ya adui.
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4 Natamani kukaa hemani mwako milele, na kukimbilia chini ya uvuli wa mbawa zako.
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
5 Ee Mungu, kwa kuwa umesikia nadhiri zangu, umenipa urithi wa wale wanaoliogopa jina lako.
Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
6 Mwongezee mfalme siku za maisha yake, miaka yake kwa vizazi vingi.
Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
7 Yeye na atawazwe kwenye kiti cha enzi mbele za Mungu milele; amuru upendo wako na uaminifu wako vimlinde.
Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
8 Ndipo daima nitaliimbia sifa jina lako na kuzitimiza nadhiri zangu siku baada ya siku.
Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.

< Zaburi 61 >