< Zaburi 26 >

1 Zaburi ya Daudi. Ee Bwana, nithibitishe katika haki, maana nimeishi maisha yasiyo na lawama; nimemtumainia Bwana bila kusitasita.
Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
2 Ee Bwana, unijaribu, unipime, uuchunguze moyo wangu na mawazo yangu;
Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
3 kwa maana upendo wako uko mbele yangu daima, nami natembea siku zote katika kweli yako.
gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
4 Siketi pamoja na watu wadanganyifu, wala siandamani na wanafiki,
Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
5 ninachukia kusanyiko la watenda mabaya na ninakataa kuketi pamoja na waovu.
na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
6 Ninanawa mikono yangu kwa kuwa sina hatia, naikaribia madhabahu yako, Ee Bwana,
Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
7 nikitangaza sifa yako kwa sauti kubwa, huku nikisimulia matendo yako ya ajabu.
ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 Ee Bwana, naipenda nyumba yako mahali unakoishi, mahali ambapo utukufu wako hukaa.
Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
9 Usiiondoe nafsi yangu pamoja na watenda dhambi, wala uhai wangu pamoja na wamwagao damu,
Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
10 ambao mikononi mwao kuna mipango miovu, ambao mikono yao ya kuume imejaa rushwa.
waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
11 Bali mimi ninaishi maisha yasiyo na lawama; nikomboe na unihurumie.
Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
12 Miguu yangu imesimama katika uwanja tambarare; katika kusanyiko kuu nitamsifu Bwana.
Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.

< Zaburi 26 >