< Zaburi 115 >
1 Sio kwetu sisi, Ee Bwana, sio kwetu sisi, bali utukufu ni kwa jina lako, kwa sababu ya upendo na uaminifu wako.
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Kwa nini mataifa waseme, “Yuko wapi Mungu wao?”
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Mungu wetu yuko mbinguni, naye hufanya lolote limpendezalo.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Lakini sanamu zao ni za fedha na dhahabu, zilizotengenezwa kwa mikono ya wanadamu.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Zina vinywa, lakini haziwezi kusema, zina macho, lakini haziwezi kuona;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 zina masikio, lakini haziwezi kusikia, zina pua, lakini haziwezi kunusa;
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 zina mikono, lakini haziwezi kupapasa, zina miguu, lakini haziwezi kutembea; wala koo zao haziwezi kutoa sauti.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Wale wanaozitengeneza watafanana nazo, vivyo hivyo wale wote wanaozitumainia.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Ee nyumba ya Israeli, mtumainini Bwana, yeye ni msaada na ngao yao.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Ee nyumba ya Aroni, mtumainini Bwana, yeye ni msaada na ngao yao.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Ninyi mnaomcha, mtumainini Bwana, yeye ni msaada na ngao yao.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 Bwana anatukumbuka na atatubariki: ataibariki nyumba ya Israeli, ataibariki nyumba ya Aroni,
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 atawabariki wale wanaomcha Bwana, wadogo kwa wakubwa.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Bwana na awawezeshe kuongezeka, ninyi na watoto wenu.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Mbarikiwe na Bwana Muumba wa mbingu na dunia.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Mbingu zilizo juu sana ni mali ya Bwana, lakini dunia amempa mwanadamu.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 Sio wafu wanaomsifu Bwana, wale washukao mahali pa kimya,
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 bali ni sisi tunaomtukuza Bwana, sasa na hata milele. Msifuni Bwana.
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.