< Zaburi 111 >

1 Msifuni Bwana. Nitamtukuza Bwana kwa moyo wangu wote, katika baraza la wanyofu na katika kusanyiko.
Yabi Ubangiji. Zan ɗaukaka Ubangiji da dukan zuciyata a cikin majalisar masu aikata gaskiya da kuma a cikin taro.
2 Kazi za Bwana ni kuu, wote wanaopendezwa nazo huzitafakari.
Ayyukan Ubangiji da girma suke; dukan waɗanda suke farin ciki da su suna tunaninsu.
3 Kazi zake zimejaa fahari na utukufu, haki yake hudumu daima.
Ayyukansa masu ɗaukaka da kuma daraja ne, adalcinsa kuma zai dawwama har abada.
4 Amefanya maajabu yake yakumbukwe, Bwana ni mwenye neema na huruma.
Ya sa a tuna da abubuwa masu banmamaki nasa; Ubangiji mai alheri ne mai tausayi kuma.
5 Huwapa chakula wale wanaomcha, hulikumbuka agano lake milele.
Yana ba da abinci ga waɗanda suke tsoronsa; yakan tuna da alkawarinsa har abada.
6 Amewaonyesha watu wake uwezo wa kazi zake, akiwapa nchi za mataifa mengine.
Ya nuna wa mutanensa ikon ayyukansa, yana ba su ƙasashen waɗansu al’ummai.
7 Kazi za mikono yake ni za uaminifu na haki, mausia yake yote ni ya kuaminika.
Ayyukan hannuwansa masu aminci ne da kuma gaskiya; dukan farillansa abin dogara ne.
8 Zinadumu milele na milele, zikifanyika kwa uaminifu na unyofu.
Tsayayyu ne har abada abadin, ana yinsu cikin aminci da kuma gaskiya.
9 Aliwapa watu wake ukombozi, aliamuru agano lake milele: jina lake ni takatifu na la kuogopwa.
Yana ba da ceto ga mutanensa; ya kafa alkawarinsa har abada, tsarki da banrazana ne sunansa.
10 Kumcha Bwana ndicho chanzo cha hekima, wote wanaozifuata amri zake wana busara. Sifa zake zadumu milele.
Tsoron Ubangiji ne mafarin hikima; dukan waɗanda suke bin farillansa suna da ganewa mai kyau. Gare shi ne madawwamin yabo.

< Zaburi 111 >