< Zaburi 106 >
1 Msifuni Bwana. Mshukuruni Bwana, kwa kuwa ni mwema; upendo wake wadumu milele.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Ni nani awezaye kusimulia matendo makuu ya Bwana au kutangaza kikamilifu sifa zake?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Heri wale wanaodumisha haki, ambao daima wanafanya yaliyo mema.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Ee Bwana, unikumbuke unapowatendea mema watu wako, uwe msaada wangu unapowaokoa,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 ili niweze kufurahia mafanikio ya wateule wako, niweze kushiriki katika furaha ya taifa lako, na kuungana na urithi wako katika kukusifu.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Tumetenda dhambi, kama vile baba zetu walivyotenda, tumekosa na tumetenda uovu.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Wakati baba zetu walipokuwa Misri, hawakuzingatia maajabu yako, wala hawakukumbuka wingi wa fadhili zako, bali waliasi kando ya bahari, Bahari ya Shamu.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Hata hivyo aliwaokoa kwa ajili ya jina lake, ili apate kudhihirisha uweza wake mkuu.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Alikemea Bahari ya Shamu, nayo ikakauka, akawaongoza katika vilindi vyake kama vile jangwani.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Aliwaokoa mikononi mwa adui; kutoka mikononi mwa adui aliwakomboa.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Maji yaliwafunika adui zao, hakunusurika hata mmoja.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Ndipo walipoamini ahadi zake, nao wakaimba sifa zake.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Lakini mara walisahau aliyowatendea, wala hawakungojea shauri lake.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Jangwani walitawaliwa na tamaa zao, walimjaribu Mungu nyikani.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Kwa hiyo aliwapa kile walichoomba, lakini akatuma juu yao ugonjwa wa kudhoofisha.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Kambini walimwonea wivu Mose, na pia Aroni aliyekuwa amewekwa wakfu kwa Bwana.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Ardhi ilifunguka ikawameza Dathani, ikawazika Abiramu na kundi lake.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Moto uliwaka katikati ya wafuasi wao, mwali wa moto uliwateketeza waovu.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Huko Horebu walitengeneza ndama, na kuabudu sanamu ya kusubu kwa chuma.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Waliubadilisha Utukufu wao kwa sanamu ya fahali, ambaye hula majani.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Walimsahau Mungu aliyewaokoa, aliyekuwa ametenda mambo makuu huko Misri,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 miujiza katika nchi ya Hamu na mambo ya kutisha huko Bahari ya Shamu.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Kwa hiyo alisema kwamba angewaangamiza: kama Mose mteule wake, asingesimama kati yao na Mungu kuizuia ghadhabu yake kuwaangamiza.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Kisha waliidharau ile nchi nzuri, hawakuiamini ahadi yake.
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 Walinungʼunika ndani ya mahema yao, wala hawakumtii Bwana.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Kwa hiyo akaapa kwa mkono ulioinuliwa kwamba atawafanya waanguke jangwani,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 kuwatawanya wazao wao waanguke miongoni mwa mataifa, na kuwatawanya katika nchi zote.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Walijifunga nira na Baali wa Peori, wakala dhabihu zilizotolewa kwa miungu isiyo na uhai.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Waliichochea hasira ya Bwana, wakamkasirisha kwa matendo yao maovu, nayo tauni ikazuka katikati yao.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Lakini Finehasi alisimama na kuingilia kati, nayo tauni ikazuiliwa.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Hili likahesabiwa kwake haki, kwa vizazi visivyo na mwisho vijavyo.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Kwenye maji ya Meriba, walimkasirisha Bwana, janga likampata Mose kwa sababu yao;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 kwa maana walimwasi Roho wa Mungu, na maneno yasiyofaa yakatoka midomoni kwa Mose.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Hawakuyaangamiza yale mataifa kama Bwana alivyowaagiza,
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 bali walijichanganya na mataifa na wakazikubali desturi zao.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Waliabudu sanamu zao, zikawa mtego kwao.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Wakawatoa wana wao na binti zao dhabihu kwa mashetani.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Walimwaga damu isiyo na hatia, damu za wana wao na binti zao, ambao waliwatoa dhabihu kwa sanamu za Kanaani, nayo nchi ikanajisika kwa damu zao.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Wakajinajisi wenyewe kwa yale waliyotenda; kwa matendo yao wenyewe wakajifanyia ukahaba.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Kwa hiyo Bwana akawakasirikia watu wake na akauchukia sana urithi wake.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Akawakabidhi kwa mataifa na adui zao wakawatawala.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Adui zao wakawaonea na kuwatia chini ya mamlaka yao.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Mara nyingi aliwaokoa lakini walikuwa wamezama kwenye uasi, nao wakajiharibu katika dhambi zao.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Lakini akaangalia mateso yao wakati aliposikia kilio chao;
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 kwa ajili yao akakumbuka agano lake, na kutokana na upendo wake mkuu akapooza hasira yake.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Akawafanya wahurumiwe na wote waliowashikilia mateka.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Ee Bwana Mungu wetu, tuokoe. Tukusanye tena kutoka kwa mataifa, ili tuweze kulishukuru jina lako takatifu, na kushangilia katika sifa zako.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Atukuzwe Bwana, Mungu wa Israeli, tangu milele na hata milele. Watu wote na waseme, “Amen!” Msifuni Bwana.
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.