< Mithali 8 >
1 Je, hekima haitani? Je, ufahamu hapazi sauti?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Juu ya miinuko karibu na njia, penye njia panda, ndipo asimamapo;
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 kando ya malango yaelekeayo mjini, kwenye maingilio, hulia kwa sauti kubwa, akisema:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 “Ni ninyi wanaume, ninaowaita; ninapaza sauti yangu kwa wanadamu wote.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Ninyi ambao ni wajinga, pateni akili; ninyi mlio wapumbavu, pateni ufahamu.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Sikilizeni, kwa maana nina mambo muhimu ya kusema; ninafungua midomo yangu kusema lililo sawa.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Kinywa changu husema lililo kweli, kwa maana midomo yangu huchukia uovu.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Maneno yote ya kinywa changu ni haki; hakuna mojawapo lililopotoka wala ukaidi.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Kwa wenye kupambanua yote ni sahihi; hayana kasoro kwa wale wenye maarifa.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Chagua mafundisho yangu badala ya fedha, maarifa badala ya dhahabu safi,
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 kwa maana hekima ina thamani kuliko marijani na hakuna chochote unachohitaji kinacholingana naye.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 “Mimi hekima, nakaa pamoja na busara; ninamiliki maarifa na busara.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 Kumcha Bwana ni kuchukia uovu; ninachukia kiburi na majivuno, tabia mbaya na mazungumzo potovu.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Ushauri na hukumu sahihi ni vyangu; nina ufahamu na nina nguvu.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Kwa msaada wangu wafalme hutawala na watawala hutunga sheria zilizo za haki,
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 kwa msaada wangu wakuu hutawala, na wenye vyeo wote watawalao dunia.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Nawapenda wale wanipendao, na wale wanitafutao kwa bidii wataniona.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Utajiri na heshima viko kwangu, utajiri udumuo na mafanikio.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Tunda langu ni bora kuliko dhahabu safi; kile nitoacho hupita fedha iliyo bora.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Natembea katika njia ya unyofu katika mapito ya haki,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 nawapa utajiri wale wanipendao na kuzijaza hazina zao.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 “Bwana aliniumba mwanzoni mwa kazi yake, kabla ya matendo yake ya zamani;
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 niliteuliwa tangu milele, tangu mwanzoni, kabla ya dunia kuumbwa.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Wakati hazijakuwepo bahari, nilikwishazaliwa, wakati hazijakuwepo chemchemi zilizojaa maji;
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 kabla milima haijawekwa mahali pake, kabla vilima havijakuwepo, nilikwishazaliwa,
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 kabla hajaumba dunia wala mashamba yake au vumbi lolote la dunia.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Nilikuwepo alipoziweka mbingu mahali pake, wakati alichora mstari wa upeo wa macho juu ya uso wa kilindi,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 wakati aliweka mawingu juu na kuziweka imara chemchemi za bahari,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 wakati aliiwekea bahari mpaka wake ili maji yasivunje agizo lake, na wakati aliweka misingi ya dunia.
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 Wakati huo nilikuwa fundi stadi kando yake. Nilijazwa na furaha siku baada ya siku, nikifurahi daima mbele zake,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 nikifurahi katika dunia yake yote nami nikiwafurahia wanadamu.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 “Basi sasa wanangu, nisikilizeni; heri wale wanaozishika njia zangu.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Sikilizeni mafundisho yangu mwe na hekima; msiyapuuze.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Heri mtu yule anisikilizaye mimi, akisubiri siku zote malangoni mwangu, akingoja kwenye vizingiti vya mlango wangu.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Kwa maana yeyote anipataye mimi amepata uzima na kujipatia kibali kutoka kwa Bwana.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Lakini yeyote ashindwaye kunipata hujiumiza mwenyewe; na wote wanichukiao mimi hupenda mauti.”
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”