< Mithali 23 >
1 Uketipo kula chakula na mtawala, angalia vyema kile kilicho mbele yako,
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 na utie kisu kooni mwako kama ukiwa mlafi.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Usitamani vyakula vyake vitamu kwa kuwa chakula hicho ni cha hila.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Usijitaabishe ili kuupata utajiri, uwe na hekima kuonyesha kujizuia.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Kufumba na kufumbua utajiri hutoweka, huwa kama umepata mabawa ghafula, ukaruka na kutoweka angani kama tai.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Usile chakula cha mtu mchoyo, usitamani vyakula vyake vitamu,
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 kwa maana yeye ni aina ya mtu ambaye kila mara anafikiri juu ya gharama. Anakuambia, “Kula na kunywa,” lakini moyo wake hauko pamoja nawe.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Utatapika kile kidogo ulichokula, nawe utakuwa umepoteza bure maneno yako ya kumsifu.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Usizungumze na mpumbavu, kwa maana atadhihaki hekima ya maneno yako.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Usisogeze jiwe la mpaka wa zamani wala kunyemelea kwenye mashamba ya yatima,
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 kwa kuwa Mtetezi wao ni mwenye nguvu, atalichukua shauri lao dhidi yako.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Elekeza moyo wako kwenye mafundisho na masikio yako kwenye maneno ya maarifa.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Usimnyime mtoto adhabu, ukimwadhibu kwa fimbo, hatakufa.
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Mwadhibu kwa fimbo na kuiokoa nafsi yake kutoka mautini. (Sheol )
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
15 Mwanangu, kama moyo wako una hekima, basi moyo wangu utafurahi,
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 utu wangu wa ndani utafurahi, wakati midomo yako itakapozungumza lililo sawa.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Usiuruhusu moyo wako kuwaonea wivu wenye dhambi, bali kila mara uwe na bidii katika kumcha Bwana.
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 Hakika kuna tumaini la baadaye kwa ajili yako, nalo tarajio lako halitakatiliwa mbali.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Sikiliza, mwanangu na uwe na hekima, weka moyo wako kwenye njia iliyo sawa.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Usiwe miongoni mwa wanywao mvinyo, au wale walao nyama kwa pupa,
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 kwa maana walevi na walafi huwa maskini, nako kusinzia huwavika matambara.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Msikilize baba yako, aliyekuzaa, wala usimdharau mama yako atakapokuwa mzee.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Nunua kweli wala usiiuze, pata hekima, adabu na ufahamu.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 Baba wa mwenye haki ana furaha kubwa, naye aliye na mwana mwenye hekima humfurahia.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Baba yako na mama yako na wafurahi, mama aliyekuzaa na ashangilie!
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Mwanangu, nipe moyo wako, macho yako na yafuate njia zangu,
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 kwa maana kahaba ni shimo refu na mwanamke mpotovu ni kisima chembamba.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 Kama mnyangʼanyi, hungojea akivizia, naye huzidisha wasio waaminifu miongoni mwa wanaume.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Ni nani mwenye ole? Ni nani mwenye huzuni? Ni nani mwenye ugomvi? Ni nani mwenye malalamiko? Ni nani aliye na majeraha yasiyo na sababu? Ni nani mwenye macho mekundu?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 Ni hao wakaao sana kwenye mvinyo, hao waendao kuonja mabakuli ya mvinyo uliochanganywa.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Usiukodolee macho mvinyo wakati ukiwa mwekundu, wakati unapometameta kwenye bilauri, wakati ushukapo taratibu!
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Mwishowe huuma kama nyoka na kutia sumu yake kama nyoka mwenye sumu.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Macho yako yataona mambo mageni na moyo wako kuwazia mambo yaliyopotoka.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 Utakuwa kama alalaye katikati ya bahari, alalaye juu ya kamba ya merikebu.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 Utasema, “Wamenipiga lakini sikuumia! Wamenichapa, lakini sisikii! Nitaamka lini ili nikanywe tena?”
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”