< Mithali 22 >
1 Heri kuchagua jina jema kuliko utajiri mwingi, kuheshimiwa ni bora kuliko fedha au dhahabu.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 Tajiri na maskini wanafanana kwa hili: Bwana ni Muumba wao wote.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 Mtu mwenye busara huona hatari na kujificha, bali mjinga huendelea mbele kama kipofu nayo ikamtesa.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 Unyenyekevu na kumcha Bwana huleta utajiri, heshima na uzima.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Katika mapito ya waovu kuna miiba na mitego, bali yeye ailindaye nafsi yake hukaa mbali nayo.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Mfundishe mtoto njia impasayo kuiendea, naye hataiacha hata akiwa mzee.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 Matajiri huwatawala maskini naye akopaye ni mtumwa wa akopeshaye.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 Yeye aupandaye uovu huvuna taabu, nayo fimbo ya ghadhabu yake itaangamizwa.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 Mtu mkarimu yeye mwenyewe atabarikiwa kwa kuwa hushiriki chakula chake na maskini.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Mfukuze mwenye dhihaka, na mvutano utatoweka; ugomvi na matukano vitakoma.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 Yeye apendaye moyo safi na yeye ambaye maneno yake ni ya neema, mfalme atakuwa rafiki yake.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 Macho ya Bwana hulinda maarifa, bali huyapinga maneno ya asiye mwaminifu.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 Mvivu husema, “Yuko simba nje!” au, “Nitauawa katika mitaa!”
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 Kinywa cha mwanamke kahaba ni shimo refu; yeye aliye chini ya ghadhabu ya Bwana atatumbukia ndani yake.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 Upumbavu umefungwa ndani ya moyo wa mtoto, bali fimbo ya adhabu itaufukuzia mbali naye.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 Yeye amwoneaye maskini ili kujiongezea mali, naye ampaye tajiri zawadi, wote huwa maskini.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Tega sikio na usikie misemo ya wenye hekima, elekeza moyo wako kwenye yale nifundishayo,
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 kwa maana inapendeza unapoyahifadhi moyoni mwako na kuwa nayo yote tayari midomoni mwako.
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 Ili tumaini lako liwe katika Bwana, hata wewe, ninakufundisha leo.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 Je, sijakuandikia misemo thelathini, misemo ya mashauri na maarifa,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 kukufundisha maneno ya kweli na ya kuaminika, ili uweze kutoa majibu sahihi kwake yeye aliyekutuma?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 Usiwadhulumu maskini kwa sababu ni maskini, wala kumdhulumu mhitaji mahakamani,
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 kwa sababu Bwana atalichukua shauri lao naye atawateka wao waliowateka.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 Usifanye urafiki na mtu mwenye hasira ya haraka, usishirikiane na yule aliye mwepesi kukasirika,
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 la sivyo utajifunza njia zake na kujiingiza mwenyewe kwenye mtego.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 Usiwe mwenye kupana mikono katika rehani, au kuweka dhamana kwa ajili ya madeni.
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 Kama ukikosa njia ya kulipa, kitanda chako kitachukuliwa ukiwa umekilalia.
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 Usisogeze jiwe la mpaka wa zamani lililowekwa na baba zako.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 Je, unamwona mtu stadi katika kazi yake? Atahudumu mbele ya wafalme; hatahudumu mbele ya watu duni.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.