< Mithali 21 >

1 Moyo wa mfalme uko katika mkono wa Bwana; huuongoza kama mkondo wa maji, popote apendapo.
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
2 Njia zote za mwanadamu huonekana sawa kwake, bali Bwana huupima moyo.
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
3 Kufanya yaliyo sawa na haki inakubalika zaidi kwa Bwana kuliko dhabihu.
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
4 Macho ya kudharau na moyo wa kiburi, ambavyo ni taa ya waovu, vyote ni dhambi!
Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
5 Mipango ya mwenye bidii huelekeza kwenye faida, kama vile kwa hakika pupa huelekeza kwenye umaskini.
Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
6 Mali iliyopatikana kwa ulimi wa uongo ni mvuke upitao upesi na mtego wa kufisha.
Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
7 Jeuri ya waovu itawaburuta mbali, kwa kuwa wanakataa kufanya yaliyo sawa.
Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
8 Njia ya mwenye hatia ni ya upotovu, bali tabia ya mtu asiye na hatia ni nyofu.
Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
9 Ni afadhali kuishi pembeni mwa paa la nyumba, kuliko kuishi nyumba moja na mke mgomvi.
Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
10 Mtu mwovu hutamani sana ubaya, jirani yake hapati huruma kutoka kwake.
Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
11 Wakati mwenye mzaha ameadhibiwa, mjinga hupata hekima; wakati mtu mwenye hekima afundishwapo, hupata maarifa.
Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
12 Mwenye Haki huyajua yanayotendeka katika nyumba za waovu, naye atawaangamiza waovu.
Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
13 Mtu akiziba masikio asisikie kilio cha maskini, yeye pia atalia, wala hatajibiwa.
In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
14 Zawadi itolewayo kwa siri hutuliza hasira na rushwa iliyofichwa kwenye nguo hutuliza ghadhabu kali.
Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
15 Wakati haki imetendeka, huleta furaha kwa wenye haki, bali kitisho kwa watenda mabaya.
Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
16 Mtu anayepotea kutoka mapito ya ufahamu, hupumzika katika kundi la waliokufa.
Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
17 Mtu apendaye anasa atakuwa maskini, yeyote apendaye mvinyo na mafuta kamwe hatakuwa tajiri.
Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
18 Waovu huwa fidia kwa ajili ya wenye haki, nao wasio waaminifu kwa ajili ya wanyofu.
Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
19 Ni afadhali kuishi jangwani kuliko kuishi na mke mgomvi na mkorofi.
Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
20 Katika nyumba ya mwenye hekima kuna akiba ya vyakula vizuri na mafuta, lakini mtu mpumbavu hutafuna vyote alivyo navyo.
A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
21 Yeye afuatiaye haki na upendo hupata uzima, mafanikio na heshima.
Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
22 Mtu mwenye hekima huushambulia mji wa wenye nguvu, na kuangusha ngome wanazozitegemea.
Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
23 Yeye alindaye kinywa chake na ulimi wake hujilinda na maafa.
Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
24 Mtu mwenye kiburi na majivuno, “Mdhihaki” ndilo jina lake; hutenda mambo kwa kiburi kilichozidi.
Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
25 Kutamani sana kwa mvivu kutakuwa kifo chake, kwa sababu mikono yake haitaki kufanya kazi.
Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
26 Mchana kutwa hutamani zaidi, lakini mnyofu hutoa pasipo kuzuia.
Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
27 Dhabihu ya mtu mwovu ni chukizo, si zaidi sana itolewapo kwa nia mbaya!
Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
28 Shahidi wa uongo ataangamia, bali maneno ya mwenye kusikia yatadumu.
Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
29 Mtu mwovu ana uso wa ushupavu, bali mtu mnyofu huzifikiria njia zake.
Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
30 Hakuna hekima, wala akili, wala mpango unaoweza kufaulu dhidi ya Bwana.
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
31 Farasi huandaliwa kwa ajili ya siku ya vita, bali ushindi huwa kwa Bwana.
Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.

< Mithali 21 >