< Ayubu 41 >

1 “Je, waweza kumvua Lewiathani kwa ndoano ya samaki, au kufunga ulimi wake kwa kamba?
“Ko za ka iya kama dodon ruwa da ƙugiyar kamar kifi ko kuma ka daure harshenta da igiya?
2 Waweza kupitisha kamba puani mwake, au kutoboa taya lake kwa kulabu?
Za ka iya sa igiya a cikin hancinta ko kuma ka huda muƙamuƙanta da ƙugiya?
3 Je, ataendelea kukuomba umhurumie? Atasema nawe maneno ya upole?
Za tă ci gaba da roƙonka ka yi mata jinƙai? Ko za tă yi maka magana a hankali?
4 Je, atafanya agano nawe ili umtwae awe mtumishi wako maisha yake yote?
Za tă yi yarjejjeniya da kai don ka ɗauke ta tă zama baiwa gare ka dukan kwanakin ranta?
5 Je, utamfuga na kumfanya rafiki kama ndege, au kumfunga kamba kwa ajili ya wasichana wako?
Za ka yi wasa da ita kamar yadda za ka yi da tsuntsu? Ko za ka daure ta da tsirkiya domin bayinka mata?
6 Je, wafanyabiashara watabadilishana bidhaa kwa ajili yake? Watamgawanya miongoni mwa wafanyao biashara?
’Yan kasuwa za su saye ta ko za su raba ta a tsakaninsu?
7 Je, waweza kuijaza ngozi yake kwa vyuma vyenye ncha kali, au kichwa chake kwa mkuki wa kuvulia samaki?
Ko za ka iya huda fatarta da kibiya ka kuma huda kansa da māsu?
8 Kama ukiweka mkono wako juu yake, utavikumbuka hivyo vita na kamwe hutarudia tena!
In ka ɗora hannunka sau ɗaya a kanta za ka tuna da yaƙin da ba za ka sāke yi ba!
9 Tumaini lolote la kumtiisha ni kujidanganya; kule kumwona tu kunamwangusha mtu chini.
Duk ƙoƙarin kama ta banza ne; ganin ta kawai abin tsoro ne.
10 Hakuna yeyote aliye mkali athubutuye kumchokoza. Ni nani basi awezaye kusimama dhidi yangu?
Ba wanda ya isa yă tsokane ta. Wane ne kuma ya isa yă yi tsayayya da ni?
11 Ni nani mwenye madai dhidi yangu ili nipate kumlipa? Kila kitu kilicho chini ya mbingu ni mali yangu.
Wane ne yake bi na bashi da dole in biya? Duk abin da yake ƙarƙashin sama nawa ne.
12 “Sitashindwa kunena juu ya maungo yake, nguvu zake na umbo lake zuri.
“Ba zan daina magana game da gaɓoɓinta ba ƙarfinta da kuma kyan kamanninta ba.
13 Ni nani awezaye kumvua gamba lake la nje? Ni nani awezaye kumsogelea na lijamu?
Wa zai iya tuɓe mata mayafinta? Wa zai iya shiga tsakanin ɓawonta.
14 Nani athubutuye kuufungua mlango wa kinywa chake, kilichozungukwa na meno yake ya kutisha pande zote?
Wa zai iya buɗe ƙofofin bakinta? Haƙoranta ma abin tsoro ne?
15 Mgongo wake una safu za ngao zilizoshikamanishwa imara pamoja;
An rufe bayanta da jerin garkuwoyi aka manne su sosai.
16 kila moja iko karibu sana na mwenzake, wala hakuna hewa iwezayo kupita kati yake.
Suna kurkusa da juna yadda da ƙyar iska take iya wucewa tsakani.
17 Zimeunganishwa imara kila moja na nyingine; zimengʼangʼaniana pamoja wala haziwezi kutenganishwa.
An haɗa su da juna sun mannu da juna kuma ba za a iya raba su ba.
18 Akipiga chafya mwanga humetameta; macho yake ni kama mionzi ya mapambazuko.
Numfashinta yana fitar da wuta; idanunta kamar hasken zuwan safe.
19 Mienge iwakayo humiminika kutoka kinywani mwake; cheche za moto huruka nje.
Wuta tana fitowa daga bakinta; tartsatsin wuta suna fitowa,
20 Moshi hufuka kutoka puani mwake, kama kutoka kwenye chungu kinachotokota kwa moto wa matete.
Hayaƙi yana fitowa daga hancinta kamar daga tukunya mai tafasa a kan wutar itace.
21 Pumzi yake huwasha makaa ya mawe, nayo miali ya moto huruka kutoka kinywani mwake.
Numfashinta yana sa garwashi yă kama wuta, harshen wuta yana fita daga bakinta.
22 Nguvu hukaa katika shingo yake; utisho hutangulia mbele yake.
Akwai ƙarfi a cikin wuyanta; razana tana wucewa a gabanta.
23 Mikunjo ya nyama yake imeshikamana imara pamoja; iko imara na haiwezi kuondolewa.
Namanta yana da kauri a manne da juna; naman yana da tauri ba ya matsawa.
24 Kifua chake ni kigumu kama mwamba, kigumu kama jiwe la chini la kusagia.
Ƙirjinta yana da ƙarfi kamar dutse, da ƙarfi kamar dutsen niƙa.
25 Ainukapo, mashujaa wanaogopa; hurudi nyuma mbele yake anapokwenda kwa kishindo.
Sa’ad da ta tashi, manya suna tsorata; suna ja da baya.
26 Upanga unaomfikia haumdhuru, wala mkuki au mshale wala fumo.
Takobi ba ta iya yankanta, kibiya ko māshi ba sa iya huda ta.
27 Chuma hukiona kama unyasi, na shaba kama mti uliooza.
Ƙarfe kamar kara ne a wurinta tagulla kuma kamar ruɓaɓɓen katako ne a wurinta.
28 Mishale haimfanyi yeye akimbie; mawe ya kombeo kwake ni kama makapi.
Māsu ba su sa ta tă gudu; jifar majajjawa kamar na ciyawa ne gare ta.
29 Rungu kwake huwa kama kipande cha jani kavu; hucheka sauti za kugongana kwa mkuki.
Kulki a gare ta kamar ciyawa ne, tana dariyar wucewar māshi.
30 Sehemu zake za chini kwenye tumbo zina menomeno na mapengo kama vigae vya chungu, zikiacha mburuzo kwenye matope kama chombo chenye meno cha kupuria.
Cikinta yana rufe a ɓawo masu ƙarfi, tana kabtar ƙasa in tana tafiya.
31 Huvisukasuka vilindi kama sufuria kubwa ichemkayo, na kukoroga bahari kama chungu cha marhamu.
Tana sa zurfin kogi yă tafasa kamar tukunya, ta kuma sa teku yă zama kamar tukunyar man shafawa.
32 Anapopita nyuma yake huacha mkondo unaometameta; mtu angedhani vilindi vilikuwa na mvi.
A bayanta ya bar haske kamar zurfin ruwan da yana kumfa.
33 Hakuna chochote duniani kinacholingana naye: yeye ni kiumbe kisicho na woga.
Ba wani abu kamar ta a duniya, halitta marar tsoro.
34 Yeye huwatazama chini wale wote wenye kujivuna; yeye ni mfalme juu ya wote wenye kiburi.”
Tana rena duk masu girman kai. Ita take mulki kan duk masu girman kai.”

< Ayubu 41 >