< Ayubu 34 >

1 Kisha Elihu akasema:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 “Sikieni maneno yangu, enyi watu wenye hekima; nisikilizeni mimi, ninyi watu wenye maarifa.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Kwa kuwa sikio huyajaribu maneno kama vile ulimi uonjavyo chakula.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Tujichagulie wenyewe yaliyo sawa, nasi tujifunze pamoja yaliyo mema.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 “Ayubu anasema, ‘Mimi sina hatia, lakini Mungu ameninyima haki yangu.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Ingawa niko sawa, ninaonekana mwongo; nami ingawa sina kosa, kidonda changu hakiponi.’
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Ni mtu gani aliye kama Ayubu, anywaye dharau kama maji?
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 Ashirikianaye na watenda mabaya na kuchangamana na watu waovu.
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Kwa kuwa anasema, ‘Haimfaidi mwanadamu kitu chochote anapojitahidi kumpendeza Mungu.’
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 “Hivyo nisikilizeni mimi, ninyi watu wenye ufahamu. Kamwe Mungu hatendi uovu, Mwenyezi hafanyi kosa.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Humlipa mwanadamu kwa ajili ya lile alilotenda; huleta juu yake kile ambacho matendo yake yanastahili.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Ni jambo lisiloweza kufikiriwa kwamba Mungu angefanya makosa, kwamba Mwenyezi angepotosha hukumu.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Je, ni nani aliyemtawaza juu ya dunia? Ni nani aliyemweka kuwa mwangalizi wa ulimwengu wote?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Kama lilikuwa kusudi la Mungu, naye akaiondoa Roho yake na pumzi yake,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 wanadamu wote wangeliangamia kwa pamoja, na mtu angerudi mavumbini.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 “Kama ninyi mnaufahamu, sikieni hili; sikilizeni hili nisemalo.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Je, yeye aichukiaye haki aweza kutawala? Je, utamhukumu mwenye haki, Aliye na Nguvu Zote?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Je, si ni yeye awaambiaye wafalme, ‘Ninyi hamfai kitu,’ nao watu mashuhuri, ‘Ninyi ni waovu,’
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 yeye asiyependelea wakuu, wala haonyeshi upendeleo kwa matajiri kuliko maskini, kwa kuwa wote ni kazi ya mikono yake?
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Wanakufa ghafula, usiku wa manane; watu wanatikiswa nao hupita; wenye nguvu huondolewa bila mkono wa mwanadamu.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 “Macho yake yanazitazama njia za wanadamu; anaona kila hatua yao.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Hakuna mahali penye giza nene, wala uvuli mkubwa, ambapo watenda mabaya wanaweza kujificha.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Mungu hana haja ya kumchunguza mtu sana, ili apate kuja mbele zake kwa hukumu.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Bila kuuliza huwapondaponda wenye nguvu nyingi na kuwaweka wengine mahali pao.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Kwa sababu huyaangalia matendo yao yote, huwaondoa usiku, nao wakaangamia.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Anawaadhibu kwa ajili ya uovu wao mahali ambapo kila mmoja ataweza kuwaona,
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 kwa sababu wameacha kumfuata Mungu, nao hawakuiheshimu njia yake hata moja.
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 Wamesababisha kilio cha maskini kifike mbele zake, hivyo akasikia kilio cha wahitaji.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Lakini kama akinyamaza kimya, ni nani awezaye kumhukumu? Kama akiuficha uso wake, ni nani awezaye kumwona? Ikiwa ni taifa au mtu mmoja, kwake ni sawa,
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 ili kumzuia mtu mwovu kutawala, au wale ambao huwategea watu mitego.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 “Kama mwanadamu akimwambia Mungu, ‘Nimekosa lakini sitatenda dhambi tena.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Nifundishe nisichoweza kuona; kama nimekukosea, sitafanya hivyo tena.’
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Je basi, Mungu atakulipa kwa masharti yako, wakati wewe umekataa kutubu? Yakupasa wewe uamue, wala si mimi; sasa niambie lile ulijualo.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 “Wanadamu wenye ufahamu husema, wenye hekima wanaonisikia huniambia,
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 ‘Ayubu huongea bila maarifa; maneno yake hayana busara.’
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Laiti Ayubu angejaribiwa hadi kikomo cha mwisho, kwa sababu anajibu kama mtu mwovu!
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Kwenye dhambi yake huongeza uasi; kwa dharau hupiga makofi miongoni mwetu, na kuzidisha maneno yake dhidi ya Mungu.”
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Ayubu 34 >