< Romanos 14 >

1 Reciban bien al que es débil en la fe, y no entren en discusiones con él.
Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba.
2 Un hombre tiene fe para tomar todas las cosas como alimento: otro que es débil en fe solo toma vegetales.
Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.
3 El que come, no menosprecie al que no come; y el que no come, no juzgue al que lo hace; porque él tiene la aprobación de Dios.
Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi.
4 ¿Quién eres tú para hacerte juez del siervo de otro hombre? si queda bien o si queda mal es a su maestro que él es responsable de lo bueno o lo malo. Pero quedará bien, porque él Señor tiene poder para hacerle quedar bien.
Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 Otro caso: Este hombre pone un día antes que otro; para ese hombre son lo mismo. Cada uno debe estar convencido de lo que cree.
Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa.
6 El que guarda el día, lo guarda para el Señor; y el que toma alimento, lo toma como el Señor, porque él alaba a Dios; y el que no toma alimento, deja de tomarlas para honrar al Señor, y también alaba a Dios.
Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.
7 Ninguno de nosotros vive para sí mismo, ni muere para sí mismo.
Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa.
8 Mientras tengamos vida, estamos viviendo para el Señor; o si morimos, para él Señor morimos. Entonces si estamos viviendo, o si nuestra vida llega a su fin, somos del Señor.
Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne.
9 Y para esto, Cristo fue a la muerte y regresó, para que él sea el Señor de los muertos y de los vivos.
Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.
10 Pero tú, ¿por qué te haces el juez de tu hermano? o de nuevo, ¿por qué no respetas a tu hermano? porque todos tendremos que tomar nuestro lugar ante Dios como nuestro juez.
Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah.
11 Porque está dicho en las Sagradas Escrituras: Vivo yo, dice el Señor, a mí toda rodilla se doblará, y toda lengua confesará a Dios.
Domin a rubuce yake, “Na rantse, “inji Ubangiji”, kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah.”
12 Entonces cada uno de nosotros tendrá que dar cuenta de sí mismo a Dios.
Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah.
13 Entonces no seamos jueces el uno del otro por más tiempo, pero tengan esto en mente, de no hacer nada que sea causa de que su hermano tropiece, o que ponga en peligro su Fe.
Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.
14 Soy consciente de esto, y estoy seguro en el Señor Jesús, que nada es inmundo en sí mismo; pero para el hombre en cuya opinión es inmunda, para él es inmundo.
Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki.
15 Y si a causa de la comida tu hermano está angustiado, entonces ya no andas conforme al amor. No dejes que tu comida sea destrucción para él por quien Cristo fue a la muerte.
Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.
16 No den pues lugar, a que se hable mal de la libertad que ustedes tienen.
Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu.
17 Porque el reino de Dios no es comida ni bebida, sino justicia, paz y gozo en el Espíritu Santo.
Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.
18 Y el que en estas cosas es el siervo de Cristo, agrada a Dios y tiene la aprobación de los hombres.
Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi.
19 Entonces, vayamos detrás de las cosas que hacen la paz, y las cosas por las cuales podemos ayudarnos unos a otros a crecer espiritualmente.
Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.
20 No permitas que la obra de Dios se desvanezca por causa de la comida. Todas las cosas son ciertamente limpias; pero es malo para ese hombre que al tomar comida lo hace perder la fe a otro.
Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi.
21 Es mejor no comer carne ni vino ni hacer nada que pueda causarle a tu hermano que tropiece.
Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.
22 La fe que tienes, tenla para ti mismo delante de Dios. Feliz es el hombre que no es juzgado por eso a lo que él da su aprobación.
Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne.
23 Pero el que duda es juzgado si come, porque no lo hace con fe; y lo que no es de fe, es pecado.
Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.

< Romanos 14 >