< Apocalipsis 2 >
1 Escribe Al ángel de la iglesia en Efeso: Estas cosas dice el que tiene las siete estrellas en su mano derecha, que camina en medio de los candeleros de oro:
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.
2 Yo conozco tus obras, y de tu arduo trabajo y paciencia; y que no soportas a hombres malvados, y has puesto a prueba a los que dicen ser apóstoles y no lo son, Y los has hallado mentirosos;
Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne.
3 Y tienes el poder de esperar, y has sufrido problemas a causa de mi nombre, y no has desmayado.
Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.
4 Pero tengo esto en contra de ti, que te has alejado de tu primer amor.
Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko.
5 Así que ten en cuenta de dónde, has caído y cambia de corazón y haz las primeras obras; o iré a ti pronto, y quitaré tu candelero de su lugar, si tus corazones no son cambiados.
Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake.
6 Pero al menos tienes el mérito de odiar las obras de los nicolaítas, como yo.
Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.
7 El que tiene oído, que oiga lo que el Espíritu dice a las iglesias. Al que venciere, le daré a comer del fruto del árbol de la vida, que está en medio del paraíso de Dios.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.
8 Y escribe al ángel de la iglesia en Esmirna diga: Estas cosas dice el primero y el último, que estaba muerto y está vivo.
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.
9 Yo conozco tus obras, tengo conocimiento de tus problemas y de cuán pobre eres (pero en realidad eres rico ) y las blasfemias de aquellos que dicen ser judíos, y no lo son, sino que son una sinagoga de Satanás.
Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne.
10 No temas las cosas que tendrás que sufrir: mira, él diablo enviará a algunos de ustedes a la cárcel, para que sean puestos a prueba; y tendrán grandes problemas por diez días. Sé fiel hasta la muerte y te daré la corona de la vida.
Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
11 El que tiene oídos, oiga lo que el Espíritu dice a las iglesias. El que venza no caerá bajo el poder de la segunda muerte.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.
12 Y escribe al ángel de la iglesia en Pérgamo: Estas cosas dice el que tiene la espada aguda de dos filos:
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.
13 Yo conozco tus obras, que tu lugar de vida es donde Satanás tiene su asiento; y tú eres fiel a mi nombre, y no has negado mi fe, incluso en los días de Antipas, mi testigo fiel, que fue muerto entre ustedes, donde Satanás tiene su lugar.
Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.
14 Pero tengo algunas cosas contra ti, porque tienes contigo a los que guardan las enseñanzas de Balaam, que enseñaba a Balac e hizo que los hijos de Israel salieran del buen camino, tomando comida que se ofrecía a dioses falsos, y a cometer fornicación.
Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci.
15 Y tienes a aquellos que guardan las enseñanzas de los Nicolaítas, la que yo aborrezco.
Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa.
16 Mira, entonces, arrepiéntete; o vendré a ti rápidamente, y haré guerra contra ellos con la espada de mi boca.
Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.
17 El que tiene oído, que oiga lo que el Espíritu dice a las iglesias. Al que venciere, le daré del maná escondido, y le daré una piedra blanca, y sobre la piedra un nombre nuevo, del cual nadie tiene conocimiento, sino aquel a quien se le da.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.
18 Y escribe al ángel de la iglesia en Tiatira: Estas cosas dice el Hijo de Dios, cuyos ojos son como llama de fuego, y sus pies como bronce pulido;
“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta, Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.
19 Yo conozco tus obras, y tu amor y tu fe y servicio paciencia, y que tus últimos trabajos son más que los primeros.
Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.
20 Pero tengo esto en contra de ti, que dejas que la mujer Jezabel, diga que es profeta y da falsas enseñanzas, y seduzca a mis siervos a fornicar y a comer la comida ofrecida a dioses falsos.
Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka.
21 Y le di tiempo para un cambio de corazón, pero ella no tiene ganas de renunciar a su inmoralidad sexual.
Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya.
22 Mira, la pondré en la cama, y a los que cometen adulterio con ella, se meterán en gran tribulación i continúan con sus obras.
Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta.
23 Y daré muerte a sus hijos; y todas las iglesias verán que yo soy el que hace la búsqueda en los pensamientos y corazones secretos de los hombres; y daré a cada uno de ustedes la recompensa de sus obras.
Zan kashe’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.
24 Pero a ustedes les digo, a los demás en Tiatira, a aquellos que no tienen esta enseñanza, y no tienen conocimiento de los secretos de Satanás, como dicen; No les impondré otra carga.
Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba.
25 Pero lo que tienes, consérvalo hasta que yo llegue.
Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’
26 El que venciere, y guardare mis obras hasta el fin, a él yo daré autoridad sobre las naciones,
Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai.
27 Y él las regirá con vara de hierro; como los vasos del alfarero serán quebrantados, como yo la he recibido de mi Padre;
‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’kamar yadda na karɓi iko daga Ubana.
28 Y le daré la estrella de la mañana.
Zan kuma ba shi tauraron asubahi.
29 El que tiene oído, que oiga lo que el Espíritu dice a las iglesias.
Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.