< Salmos 88 >
1 Oh Señor, Dios de mi salvación, te pido auxilio día y noche.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Permite que mi oración venga delante de ti; escucha mi clamor.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Porque mi alma está llena de males, y mi vida se ha acercado al inframundo. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 Soy contado entre los que descienden al sepulcro; Me he vuelto como un hombre sin fuerzas:
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Mi alma está entre los muertos, como en el infierno, a la que no le das más vueltas; porque están separados de tu cuidado. ()
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Me has puesto en las profundidades más bajas, incluso en lugares oscuros.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 El peso de tu ira me aplasta, todas tus olas me han vencido. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Has enviado a mis amigos lejos de mí; me has hecho una cosa repugnante en sus ojos: estoy encerrado y no puedo salir.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mis ojos se están consumiendo a causa de mi problema: Señor, mi llanto ha subido a ti todos los días, mis manos están extendidas hacia ti.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 ¿Harás obras de maravilla por los muertos? volverán los muertos para darte el elogio? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 ¿Se dará la historia de tu misericordia en la casa de los muertos? ¿Las noticias de tu fe llegarán al lugar de la destrucción?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 ¿Puede haber conocimiento de tus maravillas en la oscuridad? o de tu justicia en la tierra del olvido?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Pero a ti envié mi clamor, oh Señor; por la mañana mi oración vino ante ti.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Señor, ¿por qué desechas mi alma? ¿Por qué escondes de mí tu cara?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 He estado angustiado y temeroso de la muerte desde que era joven; tu ira es dura conmigo, y no tengo fuerzas.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 El ardor de tu ira me ha sobrepasado; Estoy roto, me ha vencido.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Me rodean todo el día como agua; han hecho un círculo sobre mí.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Has enviado a mis amigos y al compañero lejos de mí; Me he ido de la memoria de aquellos que son queridos por mí.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.