< Salmos 87 >
1 Esta casa está descansando en la montaña sagrada.
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 El Señor tiene más amor por las puertas de Sión que por todas las tiendas de Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Nobles cosas se dicen de ti, oh pueblo de Dios. (Selah)
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 Rahab y Babilonia serán nombrados entre los que tienen conocimiento de mí; ver, Filistea y Tiro, con Etiopía; este hombre tuvo su nacimiento allí.
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 Y de Sion se dirá: Este o aquel hombre tuvo su nacimiento allí; y el Altísimo la hará fuerte.
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 El Señor tendrá presente, cuando escriba los registros de las personas, que este hombre nació allí. (Selah)
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 Los que cantan y los que bailan, dirán: Todas mis fuentes están en ti.
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”