< Salmos 80 >

1 Escucha, oh Guardián de Israel, guiando a José como un rebaño; tú que tienes tu asiento con los ángeles. deja que se vea tu gloria.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 Delante de Efraín, de Benjamín y de Manasés, despierta de tu sueño, y ven a salvarnos.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Llévanos de nuevo, oh Dios; veamos el brillo de tu rostro y déjanos estar a salvo.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 Oh Jehová Dios de los ejércitos, ¿hasta cuándo se encenderá tu ira contra la oración de tu pueblo?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 Les diste el pan de llanto para comer; por su bebida les has dado tristeza en gran medida.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 Nos haces causa de guerra entre nuestros vecinos; nuestros enemigos se están riendo de nosotros entre ellos.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 Llévanos de nuevo, oh Dios de los ejércitos; veamos el brillo de tu rostro y déjanos estar a salvo.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 Sacaste una vid de Egipto, expulsando a las naciones y plantando en su tierra.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 Preparó un lugar para ello, para que arraigara profundamente, y envió sus ramas sobre toda la tierra.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 Las montañas estaban cubiertas con su sombra, y los grandes árboles con sus ramas.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 Envió sus armas al mar, y sus ramas al río.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 ¿Por qué derribar sus muros con tus manos, para que todos los que pasan puedan tomar su fruto?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 Es desarraigado por los cerdos del bosque, las bestias del campo obtienen su alimento de él.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Vuelve, oh Dios de los ejércitos: desde el cielo vuelven tus ojos a esta vid, y concéntrate en ella,
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 Hasta el árbol que fue plantado a tu diestra, y al árbol que para ti afirmaste.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 Se quema con fuego; es cortado: son destruidos por la ira de tu rostro.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Sea tu mano sobre el varón de tu diestra, sobre el hijo de hombre, que para ti afirmaste.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 Así no nos apartaremos de ti; guárdanos en la vida y alabaremos tu nombre.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 Llévanos, oh Jehová Dios de los ejércitos; restáuranos! veamos el brillo de tu rostro y déjanos estar a salvo.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Salmos 80 >