< Salmos 66 >

1 Emite un alegre clamor a Dios, toda la tierra:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Haz una canción en honor de su nombre: dale alabanza y gloria.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Di a Dios: ¡Cuánto temerán tus obras! debido a tu gran poder, sus enemigos se ven obligados a ponerse bajo sus pies.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Deja que toda la tierra te dé culto y te haga canciones; déjalos hacer canciones a tu nombre. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Ven y mira las obras de Dios: debe temerse en todo lo que hace a los hijos de los hombres.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 El mar se convirtió en tierra seca; atravesaron el río a pie; allí tuvimos gozo en él.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Él está gobernando en el poder para siempre; sus ojos están mirando a las naciones: que sus enemigos no tengan fuerzas contra él. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Dan bendiciones a nuestro Dios, pueblos, la voz de su alabanza sea fuerte;
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Porque él nos da vida, y no permitió que nuestros pies resbalen.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Porque tú, oh Dios, nos has puesto a prueba: probándonos con fuego como la plata.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Nos dejas encarcelar; cadenas fueron puestas en nuestras piernas.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Dejas que los hombres pasen sobre nuestras cabezas; pasamos por el fuego y el agua; pero nos sacaste a abundancia.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Entraré en tu casa con holocaustos, pagaré mi deuda contigo,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Guardando la palabra que salió de mis labios, y la cual dijo mi boca, cuando estaba en problemas.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Te daré holocaustos de animales gordos, y humo de ovejas; Haré ofrendas de bueyes y cabras. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Vengan, escúchenme, todos ustedes hombres temerosos de Dios, para que les aclare lo que él ha hecho por mi alma.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Mi voz subió a él, y fui levantado del inframundo.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Dije en mi corazón: Jehová no me escuchará:
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Pero verdaderamente el oído de Dios ha sido abierto; él ha prestado atención a la voz de mi oración.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Alabado sea Dios que no me ha quitado su buena fe y su misericordia.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Salmos 66 >