< Salmos 6 >
1 Oh Señor, no me reprendas en tu enojo; no me envíes un castigo en el calor de tu ira.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Ten piedad de mí, oh Señor, porque estoy sin fuerzas; líbrame, porque hasta mis huesos se estremecen.
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 Mi alma está muy turbada; y tú, oh Señor, ¿cuánto tiempo más tardarás?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Vuelve, oh Señor, libera mi alma; Oh dame la salvación por tu misericordia.
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 Porque en la muerte no hay memoria de ti; en el sepulcro quién te alabará? (Sheol )
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
6 Estoy cansado de llorar; toda la noche inundo mi lecho de lágrimas; riego mi cama con las gotas que fluyen de mis ojos.
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 Mis ojos se están consumiendo por tanto sufrir; están envejeciendo a causa de todos los que están en mi contra.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Apártense de mí, todos ustedes hacedores del mal; porque el Señor ha oído la voz de mi clamor.
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 El Señor ha escuchado mi petición; el Señor ha permitido que mi oración venga delante de él.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Sean avergonzados y turbados todos los que están contra mí; déjenlos retroceder y de repente se avergüencen.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.