< Salmos 56 >
1 Ten piedad de mí, oh Dios, porque el hombre está intentando destruirme; todos los días hace crueles ataques en mi contra.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Mis enemigos están siempre listos para darme fin; muchos son los que me atacan con altanería.
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 En el tiempo de mi temor, confío en ti.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 En Dios daré alabanza a su palabra; en Dios he puesto mi esperanza; No tendré miedo; qué puede hacerme el hombre?
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 Todos los días me hieren con palabras; todos sus pensamientos están en mi contra para mal.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 Se juntan, esperan en lugares secretos, toman nota de mis pasos, esperando el momento de matarme.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 Por su propia maldad no se librarán del castigo. En tu ira, oh Dios, que los pueblos sean humillados.
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 Tu llevas en cuenta mis huidas; tú recoges cada una de mis lágrimas; ¿no están en tu registro?
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 Cuando envío mi clamor a ti, mis enemigos serán vueltos atrás; Estoy seguro de esto, porque Dios está conmigo.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 En Dios daré alabanza a su palabra; en el Señor daré alabanza a su palabra.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 En Dios he puesto mi esperanza, no tendré temor; que puede hacerme el hombre?
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 Guardo el recuerdo de mi deuda contigo, oh Dios; Te daré las ofrendas de alabanza.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 Porque has librado mi alma del poder de la muerte; y que mis pies cayeran, para poder estar caminando delante de Dios en la luz de la vida.
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.