< Salmos 50 >
1 El Dios de los dioses, el Señor, ha enviado su voz, y la tierra está llena de temor; desde la llegada del sol hasta su descenso.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Desde Sión, el más bello de los lugares, Dios ha enviado su luz.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Nuestro Dios vendrá, y no callará; con fuego ardiendo delante de él y vientos de tormenta a su alrededor.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Convocará los cielos y a la tierra para juzgar a su pueblo.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Dejen que mis santos se reúnan conmigo; aquellos que han hecho un acuerdo conmigo por medio de ofrendas.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Y los cielos declaran su justicia; porque Dios mismo es el juez. (Selah)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Escucha, pueblo mío, a mis palabras; Oh Israel, seré testigo contra ti; Yo soy Dios, tu Dios.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 No tomaré una causa contra ti por tus ofrendas, ni por tus ofrendas quemadas, que están siempre ante mí.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 No tomaré buey de tu casa, ni macho cabríos de tus corrales;
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Porque toda bestia del bosque es mía, y el ganado en mil colinas.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Veo todas las aves de los montes, y las bestias del campo son mías.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Si tuviera necesidad de comida, no te diría a ti; porque la tierra es mía y toda su plenitud.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 ¿Debo tomar la carne del buey para mi alimento, o la sangre de las cabras para mi bebida?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Haz una ofrenda de alabanza a Dios; mantén los acuerdos que has hecho con el Altísimo;
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Invócame en el día de la angustia; Seré tu salvador, para que puedas darme gloria.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Pero al pecador, Dios le dice: ¿Qué estás haciendo, hablando de mis leyes, o tomando las palabras de mi acuerdo en tu boca?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Al ver que no tienes ningún deseo de mi enseñanza, y le das la espalda a mis palabras.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Cuando viste a un ladrón, estabas de acuerdo con él, y te uniste con los adúlteros.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Usas tu boca para mal, tu lengua a las palabras del engaño.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Dices mal de tu hermano; haces declaraciones falsas contra el hijo de tu madre.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Estas cosas has hecho, y yo no he dicho nada; te pareció que yo era uno como tú; pero te reprenderé cara a cara y voy ajustarte las cuentas.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Ahora ten esto en mente, tú que no tienes memoria de Dios, por temor a que seas aplastado bajo mi mano, sin nadie para darte ayuda:
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 El que hace una ofrenda de alabanza me glorifica; y al que es recto en sus caminos, le mostraré la salvación de Dios.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”