< Salmos 33 >

1 Alégrense en el Señor, hacedores de justicia; porque la alabanza es hermosa para los íntegros.
Ku rera da farin ciki ga Ubangiji ku adalai; daidai ne masu gaskiya su yabe shi.
2 Alaben al Señor con arpa; hacerle melodía de salterio y decacordio.
Ku yabi Ubangiji da garaya; ku yi kiɗi gare shi da molo mai tsirkiya goma.
3 Hazle una nueva canción; toquen con arte al aclamarlo.
Ku rera masa sabuwar waƙa; ku yi kiɗi da gwaninta, ku kuma yi sowa don farin ciki.
4 Porque la palabra del Señor es recta, y todas sus obras demuestran su fidelidad.
Gama maganar Ubangiji daidai ne da kuma gaskiya; yana da aminci cikin kome da yake yi.
5 Su deleite está en justicia y sabiduría; la tierra está llena de la misericordia del Señor.
Ubangiji yana ƙaunar adalci duniya ta cika da ƙaunarsa marar ƙarewa.
6 Por la palabra de Jehová fueron hechos los cielos; y todo el ejército del cielo por el aliento de su boca.
Ta wurin maganar Ubangiji aka yi sammai, rundunar taurarinsu kuwa da numfashin bakinsa.
7 Junta y almacena las aguas del mar; él mantiene en depósitos los mares profundos.
Ya tattara ruwan teku cikin tuluna; ya sa zurfafa cikin gidajen ajiya.
8 Que la tierra se llene del temor del Señor; deja que todas las personas del mundo te tengan un santo temor.
Bari dukan duniya ta ji tsoron Ubangiji; bari dukan mutanen duniya su girmama shi.
9 Porque él dio la palabra, y fue hecho; por su orden existió para siempre.
Gama ya yi magana, abu ya kuwa kasance; ya umarta, ya kuwa tsaya daram.
10 El Señor deshace los consejos de las naciones; él hace que los pensamientos de los pueblos no tengan efecto.
Ubangiji yakan soke shirye-shiryen al’ummai; yakan wofintar da manufofin mutane.
11 El propósito del Señor es eterno, los designios de su corazón continúan a través de todas las generaciones del hombre.
Amma shirye-shiryen Ubangiji kan tsaya daram har abada, manufofin zuciyarsa kuwa har dukan zamanai.
12 Feliz es la nación cuyo Dios es el Señor; y él pueblo quienes ha tomado como suyo.
Mai farin ciki ce al’ummar da Allah ne Ubangijinta, mutanen da ya zaɓa don gādonsa.
13 El Señor está mirando hacia abajo desde el cielo; él ve a todos los hijos de los hombres;
Daga sama Ubangiji ya duba ya kuwa ga dukan’yan adam;
14 Desde su morada vigila a todos los que viven en la tierra;
daga mazauninsa yana lura da dukan waɗanda suke zama a duniya,
15 Él formó el corazón de todos ellos; sus trabajos son claros para él.
shi da ya yi zukatan duka, wanda yake kula da kome da suke yi.
16 La salvación de un rey no está en poder de su ejército; un hombre fuerte no se libera con su gran fuerza.
Babu sarkin da ake ceto ta wurin yawan mayaƙansa; ba jarumin da kan kuɓuta ta wurin yawan ƙarfinsa.
17 Un caballo es una falsa esperanza; su gran poder no liberará a ningún hombre del peligro.
Dogara a kan doki don ceto banza ne; duk da yawan ƙarfinsa ba ya ceto.
18 Mira, el ojo del Señor está sobre aquellos en cuyo corazón está el temor de él, sobre aquellos en quienes la esperanza está en su misericordia;
Amma idanun Ubangiji suna a kan wanda yake tsoronsa, a kan waɗanda suke sa zuciya cikin ƙaunarsa marar ƙarewa,
19 Para guardar sus almas de la muerte; y para mantenerlos vivos en tiempos de hambre.
don yă cece su daga mutuwa ya bar su da rai a lokacin yunwa.
20 ¡Nuestras almas esperan al Señor; él es nuestra ayuda y nuestra salvación!
Muna jiran Ubangiji da bege; shi ne taimakonmu da garkuwarmu.
21 Porque en él nuestros corazones tienen alegría; en su santo nombre está nuestra esperanza.
A cikinsa zukatanmu na farin ciki, gama mun dogara cikin sunansa mai tsarki.
22 Sea tu misericordia sobre nosotros, oh Señor, mientras te esperamos.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zauna a kanmu, ya Ubangiji, ko ma da muke sa begenmu a gare ka.

< Salmos 33 >