< Salmos 20 >
1 Que el Señor te oiga en el día de la angustia; que el nombre del Dios de Jacob te defienda;
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
2 Que él te envíe ayuda desde el lugar santo, y te dé fuerzas desde Sión;
Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
3 Tenga en cuenta todas tus ofrendas y esté satisfecho con tu holocausto; (Selah)
Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
4 Puede él darte el deseo de tu corazón y lleve a cabo todos tus propósitos.
Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
5 Nos alegraremos en tu salvación, y en el nombre de nuestro Dios levantaremos nuestras banderas: que el Señor te dé todas tus peticiones.
Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
6 Ahora estoy seguro de que el Señor da la salvación a su rey; él le dará una respuesta desde su cielo santo con la fuerza de la salvación en su diestra.
Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
7 Algunos ponen su fe en carruajes y algunos en caballos; mas nosotros confiaremos en el nombre del Señor nuestro Dios.
Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
8 Ellos flaquean y caen; mas nosotros nos levantamos, seguimos firmes y estamos en pie.
Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
9 Ven a nuestra ayuda, Señor: que el Rey nos escuche cuando clamamos.
Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!