< Salmos 120 >

1 En mi angustia, mi llanto subió al Señor, y él me dio una respuesta.
Waƙar haurawa. Na yi kira ga Ubangiji cikin damuwata, ya kuwa amsa mini.
2 Oh Señor, sé el salvador de mi alma de los labios mentirosos y de la lengua del engaño.
Ka cece ni, ya Ubangiji, daga leɓuna masu ƙarya da kuma daga harsuna masu yaudara.
3 ¿Qué castigo te dará? ¿Qué más te hará él, lengua falsa?
Me zai yi maka, me kuma ya fi, ya kai harshe mai yaudara?
4 Flechas afiladas del fuerte y fuego ardiente.
Zai hukunta ku da kibiyoyi masu tsini na jarumi, tare da garwashin wuta na itacen tsintsiya.
5 La aflicción es mía porque soy extraño en Mesec, y vivo en las tiendas de Cedar.
Kaitona da nake zama a Meshek, da nake zama a ciki tentunan Kedar!
6 Mi alma ha estado viviendo por mucho tiempo con los que odian la paz.
Da daɗewa na zauna a cikin waɗanda suke ƙin salama.
7 Estoy a favor de la paz; pero cuando digo eso, están a favor de la guerra.
Ni mutum ne mai salama; amma sa’ad da na yi magana, su sai su yi ta yaƙi.

< Salmos 120 >