< Salmos 116 >
1 He entregado mi amor al Señor porque escuchó la voz de mi clamor y mi oración.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Ha permitido que mi oración venga ante él, y le invocaré él todos mis días.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Las redes de la muerte me rodeaban, y los dolores del inframundo me tenían agarrado; Estaba lleno de problemas y tristezas. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
4 Entonces oré al Señor, diciendo: Señor, saca mi alma de la angustia.
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 El Señor está lleno de gracia y justicia; Verdaderamente, él es un Dios de misericordia.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 El Señor guarda a los humildes; Fui humillado, y él fue mi salvador.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Vuelve a tu descanso, oh mi alma; porque el Señor te ha dado tu recompensa.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Has quitado mi alma del poder de la muerte, para que mis ojos no lloren, y mis pies no caigan.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Iré delante de Jehová en la tierra de los vivientes.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 Todavía tenía fe, aunque dije, estoy en un gran problema;
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Aunque dije en mi temor, Todos los hombres son falsos.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 ¿Qué le daré al Señor por todas las cosas buenas que él ha hecho por mí?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 Tomaré la copa de la salvación y alabaré el nombre del Señor.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Haré la ofrenda de mi juramento a Jehová, aun delante de todo su pueblo.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Querido a los ojos del Señor es la muerte de sus santos.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Oh Señor, verdaderamente yo soy tu siervo; Yo soy tu siervo, el hijo de tu sierva; por ti mis cuerdas han sido rotas.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Te daré una ofrenda de alabanza, y haré mi oración en el nombre del Señor.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 Haré las ofrendas de mi juramento, aun delante de todo su pueblo;
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 En la casa del Señor, incluso en Jerusalén. Alabado sea el Señor.
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.