< Números 10 >

1 Y él Señor dijo a Moisés:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Hagan dos trompetas de plata labrada a martillo, que se utilizarán para reunir a la gente y para dar la señal para mover las tiendas.
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
3 Cuando suenen, todas las personas deben reunirse con usted en la puerta de la Tienda de la reunión.
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
4 Si solo uno de ellos suena, entonces los jefes, los jefes de los miles de Israel, deben venir a ti.
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
5 Cuando suena una nota alta, las tiendas ubicadas en el lado este deben avanzar.
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
6 Al sonido de una segunda nota sonora, las tiendas en el lado sur deben avanzar: la nota alta será la señal para avanzar.
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
7 Pero cuando todas las personas se unen, la trompeta debe sonar con un toque simple.
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
8 Las trompetas deben ser sonadas por los hijos de Aarón, los sacerdotes; esta es una ley para ustedes para siempre, de generación en generación.
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
9 Y si van a la guerra en su tierra contra cualquiera que les haga mal, entonces suena la alarma de trompeta; y el Señor su Dios los tendrá en cuenta y les dará la salvación de los que están contra ustedes.
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
10 Y en los días de alegría y en tus fiestas regulares y el primer día de cada mes, que suenen las trompetas sobre sus ofrendas quemadas y sus ofrendas de paz; será un recordatorio para ustedes ante Dios: Yo soy el Señor, su Dios.
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
11 Ahora, en el segundo año, a los veinte días del segundo mes, la nube se levantó de la tienda del testigo.
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12 Y los hijos de Israel salieron de la tierra baldía del Sinaí; y la nube se posó en la tierra baldía de Paran.
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13 Avanzaron por primera vez en su viaje como el Señor había dado órdenes por medio de la mano de Moisés.
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14 Primero, la bandera de los hijos de Judá avanzó con sus ejércitos: y al frente de su ejército estaba Naason, el hijo de Aminadab.
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15 Y a la cabeza del ejército de los hijos de Isacar estaba Natanael, el hijo de Zuar.
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16 Y a la cabeza del ejército de los hijos de Zabulón estaba Eliab, hijo de Helón.
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17 Entonces la Tienda fue desarmada; y los hijos de Gersón y los hijos de Merari, quienes fueron los encargados de trasladar la Tienda, avanzaron.
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18 Entonces la bandera de los hijos de Rubén avanzó con sus ejércitos: y a la cabeza de su ejército estaba Elizur, el hijo de Sedeur.
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19 Y a la cabeza del ejército de los hijos de Simeón estaba Selumiel, el hijo de Zurisadai.
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20 A la cabeza del ejército de los hijos de Gad estaba Eliasaf, el hijo de Deuel.
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21 Entonces los de Coat avanzaron con el lugar santo; Los otros pusieron la Tienda lista para su llegada.
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22 Entonces la bandera de los hijos de Efraín avanzó con sus ejércitos: y a la cabeza de su ejército estaba Elisama, el hijo de Amiud.
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23 A la cabeza del ejército de los hijos de Manasés estaba Gamaliel, el hijo de Pedasur.
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24 A la cabeza del ejército de los hijos de Benjamín estaba Abidan, el hijo de Gedeoni.
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25 Y la bandera de los hijos de Dan, cuyas tiendas fueron movidas por última vez, avanzó con sus ejércitos: y a la cabeza de su ejército estaba Ahiezer, el hijo de Amisadai.
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26 A la cabeza del ejército de los hijos de Aser estaba Pagiel, el hijo de Ocrán.
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27 Y ​​a la cabeza del ejército de los hijos de Neftalí estaba Ahira, el hijo de Enan.
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
28 Este fue el orden en que los hijos de Israel viajaban por ejércitos; cuando se ponían en marcha.
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
29 Entonces Moisés dijo a Hobab, el hijo de su suegro Reuel el madianita: Estamos viajando hacia el lugar que el Señor ha dicho, Yo se los daré; vengan con nosotros, y así será para su beneficio; porque el Señor tiene cosas buenas guardadas para Israel.
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
30 Pero él dijo: No iré contigo, volveré a la tierra de mi nacimiento y a mis parientes.
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
31 Y Moisés dijo: No te vayas de nosotros; porque ustedes conocen los lugares y serán ojos para nosotros, guiándonos a los lugares correctos en las tierras baldías para instalar nuestras tiendas.
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
32 Y si vienes con nosotros, te daremos una parte en todo lo que el Señor haga por nosotros.
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
33 Así que avanzaron el viaje de tres días desde la montaña del Señor; y el cofre del pacto del Señor fue tres días delante de ellos, en busca de un lugar de descanso para ellos;
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
34 Y de día la nube del Señor pasó sobre ellos, desde que salieron del lugar donde habían puesto sus tiendas.
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 Y cuando el cofre del pacto avanzó, Moisés dijo: Levántate, oh Señor, que los ejércitos de los que están contra ti Sean dispersados, y deja que tus enemigos huyan delante de ti.
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
36 Y cuando llegó la hora de descansar, dijo: Descansa, Señor, y regresa con los miles y miles de Israel.
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”

< Números 10 >