< Nahum 1 >

1 La palabra acerca de Nínive. El libro de la visión de Nahum de Elcos.
Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
2 Él Señor es celoso y vengador; vengador es él Señor; el Señor envía castigos a quienes están en su contra, guarda rencor a sus enemigos.
Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
3 El Señor tarda en enojarse y tiene un gran poder, y no dejará ir al pecador sin castigo; el camino del Señor está en el viento y la tormenta, y las nubes son el polvo de sus pies.
Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
4 Reprende al mar y lo seca, secando todos los ríos; Son destruidos Basán, y el Carmelo, y la flor del Líbano se marchita.
Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
5 Las montañas tiemblan a causa de él, y las colinas se derriten; la tierra se está desmoronando ante él, el mundo y todos los que están en él.
Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
6 ¿Quién puede guardar su lugar ante de su ira? ¿Y quién puede resistir el calor de su furor? Su ira se desata como el fuego y él rompe las rocas.
Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
7 El Señor es bueno, una fortaleza fuerte en el día de la angustia; y conoce a aquellos que confían en él.
Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
8 Pero como el agua que se desborda, se los llevará; él pondrá fin, conduciendo a sus enemigos a la oscuridad.
amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
9 ¿Qué tramas contra el Señor? él lo hará completa destrucción; sus enemigos no volverán a aparecer por segunda vez.
Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
10 Porque aunque son como espinas retorcidas, y ebrios con la bebida, vendrán a la destrucción como paja completamente secos.
Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
11 Uno ha salido de ti que está tramando el mal contra el Señor, consejero cuyos propósitos son perversos.
Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
12 Esto es lo que el Señor ha dicho: aunque estén listos y sean muchos; Los días de mi causa contra ti han terminado; serán cortados y pasarán. Aunque te he afligido, ya no te afligiré.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
13 Y ahora dejaré que se te rompa el yugo y se separen tus cadenas.
Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
14 El Señor ha dado una orden acerca de ti, que no tendrás descendencia que lleve tu nombre; destruiré la casa de tus dioses y arrancaré las imágenes y las imágenes de fundición; Te enterraré allí, porque es un lugar de vergüenza; porque eres completamente malvado.
Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
15 ¡Mira en las montañas los pies del que viene con buenas noticias, dando palabras de paz! Celebra tus fiestas, oh Judá, da cumplimiento a tus juramentos; porque nunca más el hombre malvado volverá a pasar por ti; él está completamente destruido.
Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.

< Nahum 1 >