< Judas 1 >

1 Judas, siervo de Jesucristo y hermano de Santiago, a los llamados de Dios que han sido santificados por Dios el Padre y se mantienen guardados en Jesucristo:
Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi:
2 Misericordia a ustedes, la paz y el amor en abundancia.
bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.
3 Amados, mientras mis pensamientos estaban llenos de una carta que les iba a enviar acerca de nuestra salvación común, era necesario que les enviara una que les pedía de todo corazón que siguieran luchando fuertemente por la fe que una vez fue entregada a los santos de una vez y para siempre.
Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari.
4 Porque ciertos hombres han venido secretamente entre ustedes, señalados anteriormente en las Sagradas Escrituras para condenación, hombres sin el temor de Dios, convirtiendo su gracia en cosa inmunda, y negando a nuestro único Maestro y Señor, Jesucristo.
Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.
5 Ahora es mi propósito recordarte, aunque una vez tuviste conocimiento de todas estas cosas, de cómo el Señor, habiendo sacado a salvo a un pueblo de Egipto, más tarde envió destrucción sobre aquellos que no creyeron;
Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba.
6 Y los ángeles que no guardaron su dignidad sino que salieron del lugar que era suyo, él ha puesto en prisiones eternas y oscura hasta el gran día del juicio. (aïdios g126)
Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a. (aïdios g126)
7 Así como Sodoma y Gomorra, y las ciudades cercanas a ellos, teniendo así, entregados a deseos inmundos y perseguidos por vicios contra la naturaleza, se han convertido en un ejemplo, sometidos al castigo del fuego eterno. (aiōnios g166)
Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. (aiōnios g166)
8 De la misma manera estos soñadores contaminan la carne, no respetan a las autoridades del Señor e insultan a los poderes superiores.
Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.
9 Cuando Miguel, uno de los principales ángeles, peleaban contra el Maligno por el cuerpo de Moisés, temiendo usar palabras violentas contra él, solo dijo: que el Señor te reprenda.
Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, “Bari Ubangiji ya tsauta maka!''
10 Pero estos hombres dicen mal sobre cosas de las que no tienen conocimiento; y las cosas de las que tienen conocimiento natural, como bestias sin razón, son la causa de su destrucción.
Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan.
11 ¡Ay de ellos! Han seguido el camino de Caín, corrieron por lucro en el error de Balaam por recompensa, y han venido a la destrucción diciendo mal contra el Señor, como Coré.
Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.
12 Estos hombres son piedras invisibles en tus fiestas de amor fraternal, cuando participan en ellas, comen y beben sin mostrar ningún respeto por los demás; pastores de sí mismos; nubes sin agua que se precipitan ante el viento, árboles desperdiciados sin fruto, dos veces muertos, arrancados de raíz,
Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa.
13 Olas violentas del mar, que arrojan como espuma su propia vergüenza, estrellas errantes para quienes la noche más oscura se guarda para siempre. (aiōn g165)
Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada. (aiōn g165)
14 El profeta Enoc, que era el séptimo después de Adán, dijo de estos hombres: El Señor vino con decenas de miles de sus santos,
Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, “Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai.
15 Para ser el juez de todos, y para tomar una decisión contra todos aquellos cuyas vidas le son desagradables. por las malas acciones que han hecho, y por todas las cosas duras que los pecadores sin temor de Dios han dicho contra él.
Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi.”
16 Estos son los hombres que causan problemas, que siempre desean el cambio, que persiguen los malos placeres, usan palabras altisonantes, respetan la posición de los hombres con la esperanza de obtener recompensas.
Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.
17 Pero ustedes, mis amados, recuerden las palabras que los apóstoles de nuestro Señor Jesucristo dijeron anteriormente,
Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da.
18 Cómo les dijeron: En los últimos días habrá hombres que, guiados por sus malos deseos, habrá burladores de cosas santas.
Sun ce maku, “A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada,”
19 Estos son los hombres que hacen divisiones, hombres con deseos naturales, que no tienen el Espíritu de Dios.
Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.
20 Pero ustedes, mis amados, edificandose sobre su santa fe y haciendo oraciones en el Espíritu Santo.
Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 Manténganse en el amor de Dios, buscando la vida eterna por la misericordia de nuestro Señor Jesucristo. (aiōnios g166)
Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada. (aiōnios g166)
22 Convence a los que tienen dudas;
Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta.
23 Y a otros salvar, sacándolos del fuego; y algunos tienen misericordia con temor, odiando incluso la ropa que es impura por la carne.
Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.
24 Y aquel que es poderoso, para cuidar de que no caigan y para presentarlos sin mancha y llenos de alegría ante su gloriosa presencia,
Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa,
25 Al único Dios Sabio nuestro Salvador, démosle gloria, la grandeza y honor, autoridad y poder, antes de todos los tiempos, ahora y siempre. Que así sea. (aiōn g165)
zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin. (aiōn g165)

< Judas 1 >