< Josué 6 >
1 Ahora bien, Jericó estaba cerrada, asegurada para defenderla de los hijos de Israel; no salían ni entraban.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 Y él Señor dijo a Josué: Mira, he entregado en tus manos a Jericó con su rey y todos sus hombres de guerra.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 Ahora, dejen que todos sus hombres de guerra hagan un círculo alrededor de la ciudad, dando vueltas alrededor una vez. Hagan esto durante seis días.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 Y que siete sacerdotes vayan ante él cofre del pacto con siete cuernos de carnero en sus manos: en el séptimo día, debes ir por el pueblo siete veces, los sacerdotes tocarán sus cuernos.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Y ante el sonido de una larga nota en los cuernos, que todos griten fuertemente; y la muralla de la ciudad se derrumbará, y toda la gente deberá avanzar.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Entonces Josué, el hijo de Nun, mandó llamar a los sacerdotes y les dijo: Tomen él cofre del pacto y deja que siete sacerdotes tomen siete cuernos en sus manos y vayan delante del cofre del pacto el Señor.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 Y dijo a la gente: Vayan adelante, rodeen la ciudad y dejen que los hombres armados vayan delante del cofre del pacto del Señor.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 Entonces, después de que Josué hubo dicho esto a la gente, los siete sacerdotes con sus siete cuernos avanzaron delante del Señor, soplando sobre sus cuernos, y el cofre del pacto del Señor fue tras ellos.
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 Y los hombres armados iban delante de los sacerdotes que estaban tocando los cuernos, y la retaguardia de la gente fue tras él cofre del pacto, mientras los sacerdotes continuaban tocando sus cuernos.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 Y a la gente Josué dio una orden, diciendo: No gritarán, ni harán sonido alguno, y no dejen salir ninguna palabra de su boca hasta el día en que yo diga: Griten fuerte; entonces den un grito fuerte.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 Hizo que el cofre del pacto del Señor diera una vuelta por el pueblo una vez; luego volvieron a las tiendas para pasar la noche.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 Y temprano en la mañana se levantó Josué, y los sacerdotes tomaron el cofre del pacto del Señor.
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 Y los siete sacerdotes con sus siete cuernos continuaron delante del cofre del pacto del Señor, tocando sus cuernos; los hombres armados fueron delante de ellos, y los hombres de guerra fue tras el arca del Señor, tocando sus cuernos.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 El segundo día marcharon alrededor del pueblo una vez, y luego regresaron a sus tiendas, y así lo hicieron durante seis días.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 Al séptimo día se levantaron temprano, al amanecer del día, y marcharon alrededor de la ciudad de la misma manera, pero ese día la rodearon siete veces.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 Y la séptima vez, al sonido de los cuernos de los sacerdotes, Josué dijo a la gente: Ahora griten fuerte; porque el Señor les ha dado el pueblo.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 Y el pueblo será sometido a la destrucción, y todo lo que en él se le dará al Señor: sólo Rahab, la mujer prostituta, y todos los que están en la casa con ella, se mantendrán a salvo, porque ella mantuvo el secreto los hombres que enviamos.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 Y en cuanto a ustedes, manténganse alejados de ciudad que él Señor ha ordenado destruir, por temor a que puedan desearlos y tomen parte de ellos, y así sean causa de una maldición y grandes problemas en las tiendas de Israel.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 Pero toda la plata y el oro y los vasos de bronce y hierro son santos para el Señor: han de entrar en la tesorería del Señor.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Entonces la gente dio un fuerte grito, y sonaron los cuernos; y al oír los cuernos, la gente dio un fuerte grito, y la pared se derrumbó, de modo que la gente subió a la ciudad, todos los hombres derecho hacia adelante, y tomaron la ciudad.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 Y pusieron todo en el pueblo a la destrucción; Hombres y mujeres, jóvenes y viejos, bueyes y ovejas y asnos, mueren a filo de espada.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 Entonces Josué dijo a los dos hombres que habían sido enviados que hicieran una búsqueda por la tierra: Entra en la casa de la mujer prostituta y sácala, y a todos los que están con ella, como tú le diste tu juramento.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 Entonces los buscadores entraron y sacaron a Rahab, a su padre, a su madre, a sus hermanos y todo lo que tenía, y ellos sacaron a toda su familia; y los sacaron de las tiendas de Israel.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Luego, después de quemar la ciudad y todo lo que había en ella, pusieron la plata y el oro y las vasijas de bronce y hierro en el almacén de la casa del Señor.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Pero Josué salvó la vida a Rahab, a la mujer prostituta, y a la familia de su padre y todo lo que ella tenía, y así se ganó un lugar de vida entre los hijos de Israel hasta el día de hoy; porque ella mantuvo a salvo a los hombres que Josué había enviado para hacer una búsqueda por la tierra.
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 Entonces Josué dio órdenes al pueblo con un juramento, diciendo: Que el hombre sea maldecido ante el Señor que pone su mano en la reedificación de este pueblo: con la pérdida de su primer hijo pondrá la primera piedra de la misma en su lugar, y con la pérdida de su hijo menor, él levantará sus puertas.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 Así que el Señor estaba con Josué; Y noticias de él fueron por toda la tierra.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.