< Josué 3 >

1 Entonces Josué se levantó temprano por la mañana y, pasando de Sitim, él y todos los hijos de Israel llegaron al Jordán y estuvieron allí durante la noche antes de pasar.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 Y al cabo de tres días, los hombres en autoridad pasaron por medio del campamento,
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 Y dieron órdenes al pueblo diciendo: Cuando vean el cofre del pacto del Señor su Dios levantado por los sacerdotes, los levitas, levántate de tus lugares y ve tras él;
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 Pero deja que haya un espacio entre ustedes y él de unos dos mil codos: no se acerquen más a él, para que puedan ver el camino que tienen que recorrer, porque no han pasado por este camino antes.
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 Y Josué dijo al pueblo: Purifíquense, porque mañana el Señor hará maravillas entre ustedes.
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 Entonces Josué dijo a los sacerdotes: Toma el cofre del pacto y pasa delante de la gente. Entonces tomaron el cofre del pacto y se pusieron delante del pueblo.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 Y Él Señor dijo a Josué: Desde ahora te daré gloria en los ojos de todo Israel, para que vean eso, como yo estaba con Moisés, así estaré contigo.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Y debes dar órdenes a los sacerdotes que toman el el cofre del pacto, tú ordena: Cuando llegues al borde de las aguas del Jordán, no vayas más allá.
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 Y Josué dijo a los hijos de Israel: Vengan a mí aquí, y escuchen las palabras del Señor su Dios.
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 Y Josué dijo: Por esto verás que el Dios vivo está entre ustedes, y que ciertamente enviará de delante de ustedes al cananeo y al hitita y al heveo y al ferezeo al gergeseo y al amorreo y al jebuseo.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Mira, el cofre del pacto del Señor de toda la tierra pasa el Jordán delante de ustedes.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Así que saca a doce hombres de las tribus de Israel, un hombre de cada tribu.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 Y cuando los pies de los sacerdotes que toman el cofre del pacto del Señor, el Señor de toda la tierra, descansen en las aguas del Jordán, las aguas del Jordán serán cortadas, y todas las aguas que fluyen de arriba, se elevarán en una ola.
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 Entonces, cuando la gente salió de sus tiendas para ir al río Jordán, los sacerdotes que tomaron el cofre del pacto estaban delante del pueblo;
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 Y cuando los que tomaron el cofre del pacto llegaron al Jordán, y los pies de los sacerdotes que tomaron el cofre del pacto tocaron el borde del agua (porque las aguas del Jordán se desbordan durante todo el tiempo del corte de grano).
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 Luego, las aguas que fluían desde lo alto se detuvieron y se elevaron en una ola muy lejos en Adán, una ciudad cerca de Saretan; y las aguas que fluyen hacia el mar de Arabá, el Mar Salado, fueron cortadas, y la gente cruzó frente a Jericó.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 Y los sacerdotes que tomaron el cofre del pacto del Señor mantuvieron sus lugares, con los pies en tierra seca en medio del Jordán, mientras que todo Israel pasó por tierra seca, hasta que toda la nación pasó el Jordán.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.

< Josué 3 >