< Josué 23 >
1 Después de mucho tiempo, cuando el Señor le había dado descanso a Israel de las guerras por todos lados, y Josué era viejo y lleno de años,
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 Josué llamó todo Israel, a sus hombres responsables, a sus jefes, a sus jueces y a sus supervisores, y les dijo: Soy viejo y lleno de años.
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 Han visto todo lo que el Señor su Dios ha hecho a todas estas naciones que se les oponían; pues el SEÑOR su Dios ha estado luchando por ustedes.
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 Les he dado a ustedes, como patrimonio de sus tribus, a todas estas naciones que aún están en la tierra, junto con las que yo he cortado, desde el Jordán hasta el Gran Mar al oeste.
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 Él Señor su Dios los enviará por la fuerza, echándoles de delante de ustedes; y deben tomar su tierra para su herencia, como el Señor su Dios les dijo.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 Así que sean muy fuertes para guardar y hacer lo que está registrado en el libro de la ley de Moisés, sin apartarse de ella ni a la derecha ni a la izquierda;
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 No tengan nada que ver con estas naciones que todavía viven entre ustedes; No permitan que sus dioses sean nombrados por ustedes no sean usados en tus juramentos; No sean sus siervos ni los adoren.
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 Pero sean fiel al Señor su Dios como lo han sido hasta este día.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 Porque el SEÑOR ha enviado de delante de ustedes naciones grandes y fuertes; y hasta ahora nadie a podido resistir ante ustedes.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 Uno de ustedes puede hacer volar a mil; porque el SEÑOR su Dios está luchando por ustedes, como él les ha dicho.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 Así que vigilen, y cuiden que tengan amor por el Señor su Dios.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 Porque si se apartan de Dios, y se unen con el resto de estas naciones que todavía están entre ustedes, casándose con ellos y viviendo con ellos y ellos con ustedes:
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 Entonces pueden estar seguros de que el Señor su Dios no continuará expulsando a estas naciones de delante de ustedes; pero se convertirán en un peligro y una causa de pecado para ustedes, un látigo para sus costados y espinos en sus ojos, hasta que seas separado de esta buena tierra que el Señor su Dios les ha dado.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 Ahora estoy a punto de recorrer el camino de toda la tierra: y ustedes han visto y están seguros, todos ustedes, en sus corazones y almas, que en todas las cosas buenas que el Señor dijo acerca de ustedes, él ha guardado su promesa con ustedes, Todo se ha hecho realidad para ustedes.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 Y verás que, como todas las cosas buenas que el Señor su Dios se comprometió a hacer por ustedes, se han cumplido, así el Señor les enviará todas las cosas malas hasta que haya completado su destrucción, y estén separados de la buena tierra que el Señor su Dios les ha dado.
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 Si el pacto del Señor su Dios, que les fue dado por sus órdenes, se rompe, y se convierten en siervos de otros dioses y les dan adoración, entonces la ira del Señor arderá contra ustedes, y serán rápidamente separados de la buena tierra que él les ha dado.
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”