< Juan 2 >

1 En el tercer día, dos personas iban a casarse en Caná, en Galilea. La madre de Jesús estaba allí:
A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can,
2 Y Jesús con sus discípulos vino como huéspedes.
aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren.
3 Cuando no tenían suficiente vino, la madre de Jesús le dijo: No tienen vino.
Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”
4 Jesús le dijo: Mujer, esto no es asunto tuyo ni mío; mi tiempo está por venir.
Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”
5 Su madre le dijo a los sirvientes: Todo lo que él te diga, hazlo.
Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
6 Había seis vasijas de piedra, cada una tomando dos o tres litros de agua, fueron colocadas allí con el propósito de lavarse, como es la tradición de los judíos.
Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.
7 Jesús dijo a los sirvientes: “llenen de agua estas ollas”. Y las llenaron hasta la cima.
Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.
8 Entonces él les dijo: “Ahora toma un poco y dáselo al dueño de la fiesta”. Entonces se lo llevaron.
Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.” Suka yi haka.
9 Después de probar el agua que ahora se había convertido en vino, el dueño de la fiesta (sin saber de dónde venía, aunque estaba claro para los sirvientes que sacaron el agua) envió al hombre recién casado,
Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya
10 y le dijo: Cada hombre primero saca su mejor vino y cuando todo ha sido suficiente, saca lo que no es tan bueno; pero has guardado el buen vino hasta ahora.
ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”
11 Este, el primero de sus milagros, Jesús lo hizo en Caná en Galilea y permitió que su gloria se viera abiertamente; y sus discípulos ponen su fe en él.
Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.
12 Después de esto, descendió a Capernaúm, con su madre, sus hermanos y sus discípulos, y estuvieron allí no más de dos o tres días.
Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna’yan kwanaki.
13 El tiempo de la Pascua de los judíos estaba cerca y Jesús subió a Jerusalén.
Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima.
14 Y allí, en el Templo, vio hombres que comerciaban con bueyes, ovejas y palomas, y vio los cambiadores de dinero en sus asientos:
A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi.
15 e hizo un látigo de cuerdas pequeñas y los sacó a todos del Templo, con las ovejas y los bueyes, enviando en todas las direcciones el pequeño dinero de los cambiadores y volcando sus mesas;
Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu.
16 Y a los que comerciaban con palomas, les dijo: Quiten estas cosas; no hagan que la casa de mi Padre sea un mercado.
Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!”
17 Y llegó a la mente de los discípulos que los Escritos dicen: él celó por tu casa me consumirá.
Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”
18 Entonces los judíos le hicieron esta pregunta: ¿Qué señal de autoridad tienes para darnos, viendo que haces estas cosas?
Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”
19 Y Jesús les dijo: Envía destrucción a este templo y lo volveré a levantar en tres días.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”
20 Los judíos dijeron: La construcción de este Templo tomó cuarenta y seis años; ¡y lo levantarás en tres días!
Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?”
21 Pero sus palabras fueron acerca de ese edificio sagrado que era su cuerpo.
Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne.
22 Entonces, cuando regresó de entre los muertos, el recuerdo de estas palabras regresó a los discípulos, y tuvieron fe en las Sagradas Escrituras y en la palabra que Jesús había dicho.
Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.
23 Mientras estaba en Jerusalén, en la fiesta de la Pascua, un gran número de personas llegó a tener fe en su nombre, después de ver los milagros que él hizo.
To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa.
24 Pero Jesús no tenía fe en ellos, porque tenía conocimiento de todos ellos.
Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane.
25 Él no tenía necesidad de ningún testimonio sobre el hombre; porque él mismo tenía conocimiento de lo que había en el hombre.
Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.

< Juan 2 >