< Juan 10 >
1 De cierto les digo, que el que no entra por la puerta principal del redil a donde están las ovejas, sino que brinca el corral, es ladrón y fugitivo.
“Hakika, Hakika, ina ce maku, wanda bai shiga ta kofa zuwa garken tumaki ba, amma ya haura ta wata hanya, wannan mutum barawo ne da dan fashi.
2 El que entra por la puerta es el pastor de las ovejas.
Wanda ya shiga ta kofa shine makiyayin tumakin.
3 El portero lo deja entrar; y las ovejas oyen su voz; él llama cada oveja por su nombre y las saca.
Mai gadin kofar zai bude masa. Tumakin suna jin muryarsa, ya na kuma kiran tumakinsa da sunayensu, ya kuma kai su waje.
4 Cuando las saca a todas, va delante de ellas, y las ovejas lo siguen, porque conocen su voz.
Bayanda ya kawo su duka a waje, yana tafiya a gabansu, sai tumakin su bi shi, domin sun san muryarsa.
5 No perseguirán a otro que no sea su pastor, sino que huirán de él, porque desconocen su voz.
Ba za su bi bako ba amma sai dai su guje shi, domin basu san muryar baki ba.”
6 En esto Jesús les estaba enseñando en forma de historia: pero lo que él dijo no estaba claro para ellos.
Yesu ya yi masu magana da wannan misali, amma basu gane wadannan abubuwa da yake gaya masu ba.
7 Entonces Jesús dijo otra vez: De cierto, de cierto te digo, que yo soy la puerta por donde pasan las ovejas.
Sai Yesu ya ce masu kuma, “Hakika, Hakika, Ina ce maku, Ni ne kofar tumaki.
8 Todos los que vinieron antes de mí son ladrones y fugitivos; pero las ovejas no les prestaron atención.
Dukan wadanda suka zo kamin ni barayi ne da yan fashi, amma tumakin ba su ji su ba.
9 Yo soy la puerta: si alguno entra por mí, tendrá salvación, será como una oveja que entra y sale, y obtendrá pastos.
Ni ne kofa, In kowa ya shiga ta wurina, zai sami ceto, zai shiga ya fita ya kuma sami wurin kiwo.
10 El ladrón viene solo para robar las ovejas y darles muerte; viene para destruirlas. Yo he venido para que tengan vida y la tengan en abundancia.
Barawo ba ya zuwa sai don ya yi sata, ya kashe, ya kuma hallakar. Na zo ne domin su sami rai su kuma same shi a yalwace.
11 Yo soy el buen pastor de las ovejas: el buen pastor da su vida por las ovejas.
Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yana bada ransa domin tumakinsa.
12 El que es guardia de paga, ve al lobo que viene y se va huyendo, lejos de las ovejas; y el lobo desciende sobre ellas y las envía en todas direcciones;
Wanda yake dan sako kuma, ba makiyayi ba, wanda ba shine mai tumakin ba, in ya ga kyarkeci na zuwa sai ya saki tumakin ya gudu. Sai kyarkecin ya dauke su ya kuma warwatsa su.
13 porque él es un sirviente, y no tiene interés en las ovejas.
Ya gudu domin shi mai aikin kudi ne kuma bai damu da tumakin ba.
14 Yo soy el buen pastor; conozco a mis ovejas, y ellas me conocen a mí,
Nine makiyayi mai kyau, na kuma san nawa, nawa kuma sun san ni.
15 Así como el Padre me conoce y yo conozco al Padre; y estoy dando mi vida por las ovejas.
Uban ya san ni, ni ma na san Uban, na kuma bada raina domin tumakin.
16 Y tengo otras ovejas que no son de este redil; seré su guía en la misma dirección, y oirán mi voz, y habrá un rebaño y un pastor.
Ina da wadansu tumaki wadanda ba na wannan garken ba. Wadannan, kuma, dole in kawo su, su ma za su ji muryata saboda za su zama garke daya da makiyayi daya.
17 Por esta razón soy amado por el Padre, porque renuncio a mi vida para poder tomarla nuevamente.
Domin wannan ne Uban yake kauna ta: Na bada raina domin in same shi kuma.
18 Nadie me la quita; Yo renuncio a mi mismo Tengo poder para abandonarla, y tengo poder para tomarla de nuevo. Estas son órdenes que tengo de mi Padre.
Babu wanda zai dauke shi daga wurina, amma ina bayar da shi da kaina. Ina da ikon bada shi, ina da iko in dauke shi kuma. Na karbi wannan umarnin daga wurin Ubana.”
19 Hubo una división entre los judíos a causa de estas palabras.
Tsattsaguwa ta sake tashi tsakanin Yahudawa domin wadannan kalmomin.
20 Y algunos de ellos dijeron: Tiene un espíritu malo y está loco; ¿Por qué le escuchan?
Dayawa a cikinsu suka ce, yana da aljani, kuma mahaukaci ne. Don me ku ke sauraronsa?”
21 Otros dijeron: Estas no son las palabras de uno que tiene un espíritu malo. ¿Es posible que un espíritu maligno haga que las personas ciegas puedan recobrar la vista?
Wadansu suka ce, wadannan ba kalmomin wanda yake da aljani ba ne. Ko mai aljani zai iya bude idanun makaho?”
22 Luego vino la fiesta de la dedicación del Templo en Jerusalén, era invierno;
Sai lokacin idin Tsarkakewa a Urushalima ya zo.
23 Y Jesús estaba caminando en el Templo, por el Pórtico de Salomón.
A lokacin damuna ne, Yesu kuwa yana tafiya a shirayi cikin haikalin Sulaimanu.
24 Entonces los judíos se le acercaron, diciendo: ¿Hasta cuándo nos mantendrás en la duda? Si tu eres el Cristo, dínoslo de una vez.
Sai Yahudawa suka zagaye shi suka ce masa, “Har yaushe ne za ka bar mu cikin shakka? In kai ne Almasihun, ka gaya mana dalla-dalla.”
25 Jesús dijo en respuesta: Lo he dicho y ustedes no creen: las obras que hago en nombre de mi Padre son testimonio de mí.
Yesu ya ce masu, “Na gaya maku, amma baku gaskata ba. Ayyukan da nake yi a cikin sunan Ubana, su ke yin shaida a kaina.
26 Pero no tienen fe porque no son mis ovejas.
Duk da haka baku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 Mis ovejas oyen mi voz, y yo las conozco, y ellas me siguen;
Tumakina suna jin murya ta; Na san su, suna kuma bi na.
28 y les doy la vida eterna; nunca vendrán a la destrucción, y nadie jamás las quitará de mi mano. (aiōn , aiōnios )
Ina ba su rai na har abada; ba za su taba mutuwa ba, babu wanda zai kwace su daga hannu na. (aiōn , aiōnios )
29 Lo que mi Padre me ha dado, es más poderoso que todos; y nadie puede quitar nada de la mano del Padre.
Ubana, wanda ya bani su, ya fi kowa girma, kuma ba mai iya kwace su daga hannun Uban.
30 Yo y mi Padre somos uno.
Ni da Uban daya ne.”
31 Entonces los judíos tomaron piedras otra vez para apedrearlo.
Sai Yahudawa suka dauki duwatsu kuma domin su jajjefe shi.
32 Jesús les dijo en respuesta: Te he permitido ver una serie de buenas obras del Padre; ¿Por cuál de esas obras me están apedreando?
Yesu ya amsa masu, “Na nuna maku kyawawan ayyuka masu yawa daga wurin Uban. Saboda wane daga cikin wadannan ayyukan kuke jefe ni?”
33 Esta fue su respuesta: no te estamos apedreando por un buen trabajo sino por blasfemia; porque siendo hombre te haces Dios.
Sai Yahudawa suka amsa masa, “ba don wani aiki mai kyau muke son mu jefe ka ba, amma don sabo, domin kai, mutum ne, amma kana mayar da kanka Allah.”
34 En respuesta, Jesús dijo: ¿No hay un dicho en su ley? Yo Dije: ¿Ustedes son dioses?
Yesu ya amsa masu, “Ba a rubuce yake a shari'arku ba, 'Na ce, “ku alloli ne”'?”
35 Si dijo que eran dioses, a quienes vino la palabra de Dios y las Escrituras no pueden ser negadas,
In ya kira su alloli, su wadanda maganar Allah ta zo gare su (kuma ba za a iya karya nassi ba),
36 ¿Has dicho de aquel a quien el Padre santificó y envió al mundo? Tus palabras son malas. porque dije, ¿soy el Hijo de Dios?
kuna gaya wa wanda Uban ya kebe ya kuma aiko cikin duniya, 'Kana sabo', domin Na ce, 'Ni dan Allah ne'?
37 Si no estoy haciendo las obras de mi Padre, no tengan fe en mí;
In ba na aikin Ubana, kada ku gaskata ni.
38 Pero si las estoy haciendo, entonces tengan fe en las obras, incluso si no creen en mí; para que puedan ver claramente y estar seguros de que el Padre está en mí y yo estoy en el Padre.
Amma, idan ina yin su, ko ba ku gaskata da ni ba, ku gaskata da ayyukan saboda ku sani, ku kuma gane cewa Uban yana ciki na, ni kuma ina cikin Uban.”
39 Entonces otra vez intentaron llevarlo; pero se escapó de ellos.
Suka sake kokarin kama shi, amma ya yi tafiyarsa, ya fita daga hannunsu.
40 Y volvió otra vez al otro lado del Jordán, al lugar donde primero dio el bautismo a Juan; y estuvo allí por un tiempo.
Ya yi tafiyarsa kuma har gaba da kogin Urdun zuwa inda Yahaya ke yin baftisma ada, ya kuma zauna a wurin.
41 Y vino a él gran número de personas, diciendo: Juan no hizo ninguna señal, pero todo lo que Juan dijo de este hombre era verdad.
Mutane masu yawa suka zo wurinsa, suka ce,”Hakika Yahaya bai yi wasu alamu ba, amma dukan abubuwan da Yahaya ya ce game da wannan mutum gaskiya ne.”
42 Y muchos creyeron en él allí.
Mutane dayawa suka bada gaskiya gare shi a wurin.