< Juan 10 >
1 De cierto les digo, que el que no entra por la puerta principal del redil a donde están las ovejas, sino que brinca el corral, es ladrón y fugitivo.
“Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma.
2 El que entra por la puerta es el pastor de las ovejas.
Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne.
3 El portero lo deja entrar; y las ovejas oyen su voz; él llama cada oveja por su nombre y las saca.
Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje.
4 Cuando las saca a todas, va delante de ellas, y las ovejas lo siguen, porque conocen su voz.
Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa.
5 No perseguirán a otro que no sea su pastor, sino que huirán de él, porque desconocen su voz.
Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.”
6 En esto Jesús les estaba enseñando en forma de historia: pero lo que él dijo no estaba claro para ellos.
Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.
7 Entonces Jesús dijo otra vez: De cierto, de cierto te digo, que yo soy la puerta por donde pasan las ovejas.
Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.
8 Todos los que vinieron antes de mí son ladrones y fugitivos; pero las ovejas no les prestaron atención.
Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne,’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba.
9 Yo soy la puerta: si alguno entra por mí, tendrá salvación, será como una oveja que entra y sale, y obtendrá pastos.
Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo.
10 El ladrón viene solo para robar las ovejas y darles muerte; viene para destruirlas. Yo he venido para que tengan vida y la tengan en abundancia.
Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.
11 Yo soy el buen pastor de las ovejas: el buen pastor da su vida por las ovejas.
“Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin.
12 El que es guardia de paga, ve al lobo que viene y se va huyendo, lejos de las ovejas; y el lobo desciende sobre ellas y las envía en todas direcciones;
Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su.
13 porque él es un sirviente, y no tiene interés en las ovejas.
Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.
14 Yo soy el buen pastor; conozco a mis ovejas, y ellas me conocen a mí,
“Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni,
15 Así como el Padre me conoce y yo conozco al Padre; y estoy dando mi vida por las ovejas.
kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin.
16 Y tengo otras ovejas que no son de este redil; seré su guía en la misma dirección, y oirán mi voz, y habrá un rebaño y un pastor.
Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma.
17 Por esta razón soy amado por el Padre, porque renuncio a mi vida para poder tomarla nuevamente.
Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma.
18 Nadie me la quita; Yo renuncio a mi mismo Tengo poder para abandonarla, y tengo poder para tomarla de nuevo. Estas son órdenes que tengo de mi Padre.
Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”
19 Hubo una división entre los judíos a causa de estas palabras.
Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa.
20 Y algunos de ellos dijeron: Tiene un espíritu malo y está loco; ¿Por qué le escuchan?
Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”
21 Otros dijeron: Estas no son las palabras de uno que tiene un espíritu malo. ¿Es posible que un espíritu maligno haga que las personas ciegas puedan recobrar la vista?
Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”
22 Luego vino la fiesta de la dedicación del Templo en Jerusalén, era invierno;
Bikin Miƙawa a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa.
23 Y Jesús estaba caminando en el Templo, por el Pórtico de Salomón.
Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon,
24 Entonces los judíos se le acercaron, diciendo: ¿Hasta cuándo nos mantendrás en la duda? Si tu eres el Cristo, dínoslo de una vez.
sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”
25 Jesús dijo en respuesta: Lo he dicho y ustedes no creen: las obras que hago en nombre de mi Padre son testimonio de mí.
Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni.
26 Pero no tienen fe porque no son mis ovejas.
Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne.
27 Mis ovejas oyen mi voz, y yo las conozco, y ellas me siguen;
Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na.
28 y les doy la vida eterna; nunca vendrán a la destrucción, y nadie jamás las quitará de mi mano. (aiōn , aiōnios )
Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. (aiōn , aiōnios )
29 Lo que mi Padre me ha dado, es más poderoso que todos; y nadie puede quitar nada de la mano del Padre.
Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana.
30 Yo y mi Padre somos uno.
Da ni da Uba ɗaya ne.”
31 Entonces los judíos tomaron piedras otra vez para apedrearlo.
Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
32 Jesús les dijo en respuesta: Te he permitido ver una serie de buenas obras del Padre; ¿Por cuál de esas obras me están apedreando?
amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”
33 Esta fue su respuesta: no te estamos apedreando por un buen trabajo sino por blasfemia; porque siendo hombre te haces Dios.
Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”
34 En respuesta, Jesús dijo: ¿No hay un dicho en su ley? Yo Dije: ¿Ustedes son dioses?
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’?
35 Si dijo que eran dioses, a quienes vino la palabra de Dios y las Escrituras no pueden ser negadas,
Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’
36 ¿Has dicho de aquel a quien el Padre santificó y envió al mundo? Tus palabras son malas. porque dije, ¿soy el Hijo de Dios?
to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’
37 Si no estoy haciendo las obras de mi Padre, no tengan fe en mí;
In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni.
38 Pero si las estoy haciendo, entonces tengan fe en las obras, incluso si no creen en mí; para que puedan ver claramente y estar seguros de que el Padre está en mí y yo estoy en el Padre.
Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.”
39 Entonces otra vez intentaron llevarlo; pero se escapó de ellos.
Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
40 Y volvió otra vez al otro lado del Jordán, al lugar donde primero dio el bautismo a Juan; y estuvo allí por un tiempo.
Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna
41 Y vino a él gran número de personas, diciendo: Juan no hizo ninguna señal, pero todo lo que Juan dijo de este hombre era verdad.
mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.”
42 Y muchos creyeron en él allí.
A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.