< Job 37 >
1 A esto me tiembla el corazón; se mueve fuera de su lugar.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Escucha el ruido de su voz; al sonido hueco que sale de su boca.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Él lo envía a través de todo el cielo, y su trueno llama hasta los confines de la tierra.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Después de esto suena una voz que truena la palabra de su poder; no retiene sus truenos; de su boca suena la voz.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Él hace maravillas, más de lo que se puede comprender; grandes cosas de las cuales no tenemos conocimiento;
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Porque dice a la nieve: Moja la tierra; Y a la tormenta de lluvia, baja.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Él pone fin a la obra de cada hombre, para que todos puedan ver su obra.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Entonces las bestias se meten en sus agujeros, y descansan.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Del sur sale el viento de tormenta y el frío del norte.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Por el aliento de Dios se hace hielo, y las anchas aguas se congelan.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 La nube espesa está cargada con una llama de trueno, y la nube emite su luz;
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Y va por este camino, dando la vuelta, girándose por su guía, para hacer lo que él ordene que se haga, en la superficie del mundo, la tierra de los hombres,
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Por corrección, o por su tierra, o por misericordia, las hará venir.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Escucha esto, oh Job, y guarda silencio en tu lugar; y toma nota de las maravillas hechas por Dios.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 ¿Tienes conocimiento del orden de Dios de sus obras, cómo hace que se vea la luz de su nube?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 ¿Tienes conocimiento como flotan las nubes, las maravillas de aquel que es perfecto en sabiduría?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Tú, cuya ropa es cálida, cuando la tierra está tranquila debido al viento del sur,
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 ¿Harás, con él, los cielos suaves y fuertes como un espejo pulido?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Dejame claro lo que debemos decirle; No podemos poner nuestra causa ante él, debido a la oscuridad.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 ¿Cómo puede él conocer mi deseo de hablar con él? ¿O algún hombre dijo alguna vez: ¿Puede la destrucción venir a mí?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Y ahora no se ve la luz, porque es oscura a causa de las nubes; Pero viene un viento que las aleja.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Una luz brillante sale del norte; La gloria de Dios es grandemente temible.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 No alcanzaremos al Todopoderoso; su fuerza y su juicio son grandes; Él está lleno de justicia, no haciendo nada malo.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Por esta causa los hombres van por temor a él; no tiene respeto por los sabios de corazón.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”