< Job 36 >
1 Y Eliu continuó diciendo:
Elihu ya ci gaba,
2 Dame un poco más de tiempo para declarar; porque todavía tengo algo que decir en defensa de Dios.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Obtendré mi conocimiento de lejos, y le daré justicia a mi Hacedor.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Porque verdaderamente mis palabras no son falsas; Uno que es perfecto en su conocimiento está hablando contigo.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 He aquí, Dios es grande, no aborrece, es poderoso en la virtud de su corazón.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 No perdona la vida al impio, y da a los oprimidos sus derechos;
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 No apartará los ojos de los justos, hasta el trono de los reyes, los afirma para siempre, exaltandolos.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Y si han sido encarcelados en cadenas, y cautivos en cuerdas de aflicción,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Entonces les deja claro lo que han hecho, incluso las obras malvadas de las que se enorgullecen.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Su oído está abierto a su enseñanza, y él les da órdenes para que sus corazones se vuelvan del mal.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 Si escuchan su voz y cumplen su palabra, entonces él les da larga vida y años llenos de placer.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 Pero si no, perecerán a espada llegan y morirán sin conocimiento.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Los que no temen a Dios mantienen la ira acumulada en sus corazones; No dan gritos de ayuda cuando son hechos prisioneros.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Llegan a su fin cuando aún son jóvenes, su vida es corta como la de aquellos que se usan con fines sexuales en la adoración de sus dioses.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Él salva al afligido en su aflicción, abriendo sus oídos en tiempos de opresión.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 También te apartará de la boca de tus adversarios, a lugar espacioso libre de angustias; te asentará mesa llena de grosura.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Pero tú has cumplido el juicio del malvado, contra la justicia y el juicio que lo sustenta todo.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Ten cuidado que en su ira no te quite con golpe, porque ni un gran rescate te libera.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Hará él estima de tus riquezas, ni tu oro ni la potencia de tu poder.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 No anheles la noche cuando la gente asciende a su lugar.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Ten cuidado, de no volverte al pecado, porque has escogido el mal, en lugar de la miseria.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Verdaderamente Dios es excelso en su potencia; ¿Quién es un maestro como él?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 ¿Quién alguna vez le dio órdenes, o le dijo, has hecho mal?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Mira que tienes que alabar su obra, sobre el cual los hombres hacen canciones.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Todas las personas la están mirando; él hombre la ve desde lejos.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 En verdad, Dios es grande, más grande que todo nuestro conocimiento; El número de sus años no pueden ser contados.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Porque toma las gotas del mar; los envía a través de su niebla como lluvia,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Que desciende del cielo y cae sobre los pueblos.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 ¿Y quién sabe cómo se extienden las nubes o los truenos de su tienda?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Mira, él está extendiendo su niebla, cubriendo con ella las cimas de las montañas.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Porque por éstos da comida a los pueblos, y pan en plena medida.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 con las nubes encubre la luz, y le manda no brillar, interponiendo aquéllas.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 El trueno deja en claro su pasión, y la tormenta da noticias de su ira.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.