< Job 31 >
1 Hice un acuerdo con mis ojos; ¿Cómo podrían mis ojos estar mirando a una virgen?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 ¿Cuál es la recompensa de Dios desde lo alto, o la herencia dada por él Todopoderoso desde el cielo?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 ¿No es problema para el pecador, y destrucción para los que hacen el mal?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 ¿No ve él mis caminos, y mis pasos no están todos numerados?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Si he ido por caminos falsos, o mi pie se apuró rápido a engaño;
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Déjame ser medido en escalas rectas, y deja que Dios vea mi justicia.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Si mis pasos han sido apartados, o si me dejado llevar por la codicia, o si la propiedad de otro está en mis manos;
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Si siembro mi semilla en la tierra para que otro tenga su fruto, y deja que mi producto sea arrancado de raíz.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Si mi corazón iba tras la esposa de otro hombre, o si esperaba en acecho la puerta de mi vecino;
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Entonces deja que mi esposa dé placer a otro hombre y que otros usen su cuerpo.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Porque eso sería un crimen; sería un acto por el cual los jueces medirían el castigo:
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Sería un fuego que arderá hasta la destrucción, y que me quitaría todo lo que tengo.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Si he desdeñado el derecho de mi sirviente, o mi sirvienta, cuando contendieron conmigo;
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 ¿Qué haré cuando Dios venga como mi juez? ¿Y qué respuesta puedo dar a sus preguntas?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 ¿No lo hizo Dios tan bien como yo? ¿No nos dio vida en los cuerpos de nuestras madres?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Si retenía el deseo de los pobres; o he hecho desfallecer los ojos de la viuda;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Si me guardaba la comida y no le daba un poco al huérfano;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 Porque desde mi juventud él creció conmigo como un padre, desde mis primeros días; y a la viuda la guié desde mi niñez;
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Si he visto a alguien cercano a la muerte por necesidad de ropa, y a los pobres sin nada que los cubriera;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 Si su espalda no me dio una bendición, y la lana de mis ovejas no lo calentó;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Si mi mano había sido levantada contra él justo, cuando vi que los jueces me apoyaban;
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Que mi brazo sea arrancado de mi cuerpo, y que sea roto desde su base.
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Porque el temor de Dios me retuvo, y debido a su poder no podría hacer tales cosas.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Si hice del oro mi esperanza, o si alguna vez dije al mejor oro, he puesto mi fe en ti;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Si me alegrara porque mi riqueza era grande, y porque mi mano había reunido mucho;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Si, cuando vi el sol brillando, y la luna moviéndose en su camino brillante,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 Un sentimiento secreto de adoración entró en mi corazón, y mi boca besó mi mano;
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Ese hubiera sido otro pecado para ser recompensado con el castigo de los jueces; porque habría sido falso a Dios en lo alto.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Si me alegré en la destrucción de mi aborrecedor, y grité de alegría cuando el mal lo alcanzó;
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Porque no dejé que mi boca cediera al pecado al poner una maldición sobre su vida?
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Si los hombres de mi tienda dijeran: ¿Quién no ha comido toda su carne, no se saciaría?
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 El viajero no tomó su descanso nocturno en la calle, y mis puertas estaban abiertas para cualquier persona en un viaje;
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Si mis malas obras cubiertas como Adan, y mi pecado en el secreto de mi pecho,
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Por temor al gran grupo de personas, o por temor a que las familias me despreciarán, para que me quede callado y no salga por mi puerta;
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 ¡Si solo Dios me escuchara, y él Todopoderoso me contestara! ¡O si lo que él tiene contra mí se hubiera puesto por escrito!
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 En verdad tomaría el libro en mis hombros; sería para mí como una corona;
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Dejaría claro el número de mis pasos, ¡lo pondría ante él como un príncipe! Las palabras de Job se acaban.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Si mi tierra ha clamado contra mí, o los surcos ha estado triste;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 Si he tomado su producto sin pago, causando la muerte de sus dueños;
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Luego, en lugar de grano, salen espinas, y en lugar de cebada, plantas malolientes. Las palabras de Job han terminado.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.