< Job 3 >

1 Entonces, abriendo su boca y maldiciendo el día de su nacimiento,
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 Job dijo:
Ayuba ya ce,
3 Perezca el día de mi nacimiento y la noche en que se dijo: Un niño es concebido.
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Que ese día, hubiera sido oscuro; y Dios no hubiera tomado nota de esto desde lo alto, y no hubiera resplandecido la luz del día;
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Deja que la oscuridad y la noche negra sea su redentor; deja que se cubra con una nube; Deja que las sombras oscuras del día te envíen miedo.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 En cuanto a esa noche que la oscuridad espesa la tome; Que no tenga gozo entre los días del año; Que no venga en el número de los meses.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 En cuanto a esa noche, que hubiera sido estéril; Que ninguna voz de alegría hubiera sonado en ella;
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Que la maldigan los que ponen una maldición en el día; que están listos para despertar a Leviatán.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Sean oscuras sus estrellas de la mañana; Que esté buscando luz, pero que no la tenga; Que no vea los rayos del alba.
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 Porque no cerró las puertas del vientre de mi madre, ni oculto los problemas de mis ojos.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 ¿Por qué la muerte no me tomó cuando salí del cuerpo de mi madre, por qué no, cuando salí del vientre, entregue mi espíritu?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 ¿Por qué hubo rodillas que me recibieron o por qué los pechos para que me den leche?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 Porque entonces podría haber ido a mi descanso en silencio, y en el sueño, haber estado en paz,
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 Con los reyes y los sabios de la tierra, que edificaron grandes casas para sí mismos;
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 O con los gobernantes que tenían oro, y cuyas casas estaban llenas de plata;
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 O como un aborto de niño que nunca podría haber existido; Como niños pequeños que no han visto la luz.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 Allí dejan de perturbar los malvados, y aquellos cuyas fuerzas han llegado a su fin tienen descanso.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Allí los prisioneros están en paz juntos. La voz del capataz no vuelve a sus oídos.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 El pequeño y el grande están allí, y el siervo está libre de su amo.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 ¿Por qué le da luz al que está en problemas, y la vida al alma amarga;
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 Para aquellos cuyo deseo es la muerte, pero no viene; que la buscan más que la riqueza secreta;
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 ¿Que se alegran con gran gozo y se regocijan cuando llegan a su último lugar de descanso;
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 Pporque se le da luz a un hombre que no sabe por donde va, y que está acorralado por Dios?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 En lugar de mi comida tengo pena, y de mí salen gritos de dolor como agua.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Porque lo que estaba temiendo ha venido sobre mi y de lo cual tengo miedo me aconteció.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 No tengo paz, ni silencio, ni descanso; nada más que el dolor viene sobre mí.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >