< Job 29 >
1 Y Job nuevamente tomó la palabra y dijo:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 ¡Si pudiera volver a ser como estaba en los meses pasados, en los días en que Dios me estaba cuidando!
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 Cuando su luz brillaba sobre mi cabeza, y cuando por su luz podía andar en la oscuridad.
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 Cuando yo estaba en los días de mi juventud, cuando mi tienda fue cubierta por la mano de Dios;
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 Cuando él Todopoderoso estaba todavía conmigo, y mis hijos me rodeaban;
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 Cuando mis pies se lavaron con leche, y ríos de aceite fluían de la roca para mí.
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 Cuando salía a la puerta, para subir al pueblo y tomar asiento en el lugar público.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 Los jóvenes me vieron y se escondían, y los ancianos se levantaron de sus asientos;
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 Los gobernantes se callaron, y se pusieron las manos en la boca;
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 Los jefes bajaron su voz, y sus lenguas se les pegaba al paladar de sus bocas.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 Porque cuando llegó a sus oídos, los hombres dijeron que yo era verdaderamente feliz; Y cuando vieron sus ojos, me dieron testimonio;
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 Porque yo era un salvador de los pobres cuando él clamaba por ayuda, y por huérfano que no tenía ayuda.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 La bendición de aquel que estaba cerca de la destrucción vino sobre mí, y puse una canción de alegría en el corazón de la viuda.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 Me puse la justicia como mi ropa, y estaba llena de ella; Las decisiones correctas fueron para mí una bata y un tocado.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Yo era ojos para los ciegos, y pies para el que no tenía poder para caminar.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 Yo era un padre para los pobres, examinaba la causa que no conocía.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 Por mí se rompieron los grandes dientes del malvado, y le hice renunciar a lo que había quitado violentamente.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Entonces dije: Terminaré con mis hijos a mi alrededor, mis días serán como la arena en número;
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 Mi raíz estará abierta a las aguas, y él rocío de la noche estará en mis ramas,
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 Mi gloria será siempre nueva, y mi arco se renueva fácilmente en mi mano.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Los hombres me escucharon, esperando y guardando silencio para mis sugerencias.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 Después de haber dicho lo que tenía en mente, se quedaron callados y dejaron que mis palabras se adentren en sus corazones;
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 Me esperaban como a la lluvia, abriendo la boca como a las lluvias de primavera.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Cuando yo les sonreía, cuando no tenían esperanza, y la luz de mi cara nunca fue nublada por su miedo.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Tomé mi lugar como jefe, guiándolos en su camino, y fui como rey entre su ejército cuando estaban tristes yo los consolaba.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.