< Job 18 >

1 Entonces Bildad el suhita respondió y dijo:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 ¿Cuánto tiempo pasará antes de que hayas terminado de hablar? muestren entendimiento, y luego diremos lo que está en nuestras mentes.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 ¿Por qué parecemos bestias y estúpidos ante tus ojos?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Tu crees que en tu enojo, que te estás desgarrando con rabia, ¿la tierra será desierta por tu culpa, o se moverá una roca de su lugar?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Porque la luz del pecador se apaga, y la llama de su fuego no brilla.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 La luz está oscura en su casa, y la luz que brilla sobre él se apaga.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Los pasos de su fuerza se vuelven cortos, y caerá en su propia trampa.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Sus pies lo llevan a la red, y él va caminando por las cuerdas.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Su pie es tomado en la red; él entra en su agarre.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 La cuerda se pone secretamente en la tierra para atraparlo, y la cuerda se coloca en su camino.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Lo superan los miedos por todos lados, lo persiguen a cada paso.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Su fuerza es debilitada por la necesidad de comida, y la destrucción está esperando su paso.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Su piel es desperdiciada por una enfermedad, le devora la carne poco a poco; él primogénito de la muerte.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Lo desarraigan de su tienda donde estaba a salvo, y se lo llevan al rey de los temores.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 En su tienda se verá lo que no es suyo, azufre se deja caer sobre su casa.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Bajo la tierra, sus raíces están secas, y sobre ella se corta su rama.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Su memoria se ha ido de la tierra, y en las calles no hay conocimiento de su nombre.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Él es enviado de la luz a la oscuridad; Él es obligado a salir del mundo.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 No tiene descendencia ni familia entre su pueblo, y en su lugar de residencia no hay nadie de su nombre.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 A su destino, los del oeste se sorprenden, y los del este son vencidos por el miedo.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 En verdad, estas son las casas del pecador, y este es el lugar de aquel que no tiene conocimiento de Dios.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >