< Job 13 >
1 Verdaderamente, mi ojo ha visto todo esto, me han llegado noticias al oído y tengo conocimiento de ello.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 En mi mente están las mismas cosas que en la tuya; Soy igual a ustedes.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Pero habría hablado con el Dios Todopoderoso, y mi deseo es tener una discusión con Dios.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Pero ustedes son forjadores de mentiras; Todos ustedes son médicos vanos, no tienen ningún valor.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 ¡Si solo te callas, sería un signo de sabiduría!
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Escucha el argumento de mi boca, y toma nota de las palabras de mis labios.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 ¿Dirás en el nombre de Dios lo que no está bien, y le pondrás palabras falsas en la boca?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 ¿Tendrán respeto por la persona de Dios en esta causa y se presentarán como sus partidarios?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 ¿Será bueno para ti ser examinado por él, o tienes el pensamiento de que puede ser guiado al error como un hombre?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Él ciertamente te castigará, si muestras preferencia por las personas en secreto.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 ¿No te hará temer su gloria para que tus corazones sean vencidos delante de él?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Tus recuerdos son solo polvo, y tus cuerpos son solo barro.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Cállense y déjenme decir lo que tengo en mente, y que venga lo que venga sobre mí.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Porque he de quitarme mi carne con mis dientes, y pondré mi vida en mis manos.
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 En verdad, él me pondrá fin; aun así esperaré en él, con tal de presentar ante el mi argumento;
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Y esa será mi salvación, porque un malvado no vendría ante él,
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Escuchen mis palabras con cuidado y mantengan lo que digo en sus mentes.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Mira, he puesto en orden mi causa y estoy seguro de que seré justificado.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 ¿Alguien puede argumentar en mi contra? Si es así, me quedaría callado y me quedaría sin vida.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Solo dos cosas quiero hacer, entonces no me esconderé de tu presencia.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Quita tu mano de mí; y no me asustes con tu terror.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Entonces, al sonido de tu voz daré respuesta; o déjame exponer mi causa para que me des una respuesta.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 ¿Cuál es el número de mis malas acciones y mi pecado? dame conocimiento de mis transgresiones y mis pecados.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 ¿Por qué tu rostro está oculto de mí, como si estuviera contado entre tus enemigos?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 ¿Serás duro con una hoja en vuelo ante el viento? ¿Perseguirás a una paja?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Porque escribes cosas amargas en mi contra, y me castigaste por los pecados de mi juventud;
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Y pones cepos en mis pies, vigilando todos mis caminos, imprimes marcas en las plantas de mis pies;
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Y él se consumirá como una cosa podrida, o como una túnica que se ha convertido en alimento para la polilla.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.