< Jeremías 33 >

1 Entonces la palabra del Señor vino a Jeremías la segunda vez, mientras él todavía estaba encerrado en el lugar de los vigilantes armados, diciendo:
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 Estas son las palabras del Señor, que hizo la tierra, el Señor que la afirmó en su sitio; el Señor es su nombre;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 Deja que tu clamor venga a mí, y te daré una respuesta, y te haré ver grandes cosas y cosas secretas de las que no tienes conocimiento.
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 Porque esto es lo que el Señor, el Dios de Israel, ha dicho acerca de las casas de este pueblo y las casas de los reyes de Judá, que se han destruido para hacer rampas y la espada.
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 Vinieron a pelear con los caldeos, pero solo servirán para llenar la ciudad con cadáveres de hombres a los que he condenado a muerte en mi ira y en mi furor, y debido a cuya maldad he mantenido el rostro cubierto de esta ciudad.
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 Mira, los sanaré, les daré la salud nuevamente, los sanaré; y les dejaré ver la paz y la verdad en abundancia.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 Y dejaré que se cambie el destino de Judá y de Israel, y los reconstruiré como al principio.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 Y los limpiaré de todos sus pecados, con los cuales han estado pecando contra mí; Tendré perdón por todos sus pecados, con los cuales ellos han estado pecando contra mí, y con los cuales han hecho el mal contra mí.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 Y este pueblo será para mí un nombre de alegría, una alabanza y una gloria ante todas las naciones de la tierra, quienes, al oír todo el bien que estoy haciendo por ellos, temblarán de miedo. Por todo el bien y la paz que estoy haciendo por ello.
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 Esto es lo que el Señor ha dicho: Se volverán a oír en este lugar, del cual dices: Es un desperdicio, sin hombres y sin animales; incluso en las ciudades de Judá y en las calles de Jerusalén, en ruinas y despobladas, sin hombre y sin animal,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 Voces felices, la voz de alegría, la voz del hombre recién casado y la voz de la novia, las voces de los que dicen: Alaben al Señor de los ejércitos, porque el Señor es bueno y su misericordia para siempre; las voces de los que van con alabanza a la casa del Señor. Porque devolveré los cautivos de la tierra para que vuelvan a ser como él principio, dice el Señor.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 Esto es lo que ha dicho el Señor de los ejércitos: Nuevamente habrá en este lugar, que es un desperdicio, sin hombre y sin animal, y en todos sus pueblos, volverá haber un lugar de descanso donde los criadores de ovejas harán sus rebaños descansar.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 En los pueblos de la región montañosa, en los pueblos de las tierras bajas, en los pueblos del sur y en la tierra de Benjamín y en los alrededores de Jerusalén y en los pueblos de Judá, los rebaños volverán a pasar bajo la mano del que los cuenta, dice el Señor.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 Mira, vienen días, dice el Señor, cuando cumpliré la buena palabra que he dicho acerca del pueblo de Israel y del pueblo de Judá.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 En aquellos días y en ese tiempo, permitiré que una Rama de justicia suba para David; y él será juez de justicia en la tierra.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 En aquellos días, Judá tendrá la salvación y Jerusalén estará segura: y este es el nombre que le será dado: El Señor es nuestra justicia.
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 Porque él Señor ha dicho: David nunca estará sin un descendiente que ocupe su lugar en el trono del reino de Israel;
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 Y los sacerdotes y los levitas nunca estarán sin un descendiente que venga ante mí, ofreciendo ofrendas quemadas, incienso ofrendas de cereales y ofrendas de bestias en todo momento.
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 Y vino la palabra del Señor a Jeremías, diciendo:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 El Señor ha dicho: Si es posible que se rompa mi pacto del día y la noche, que el día y la noche ya no lleguen a sus horas fijas,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 Entonces mi pacto con mi siervo David puede romperse, de modo que ya no tenga un hijo para ocupar su lugar en el asiento del reino; y mi pacto con los levitas, los sacerdotes, mis siervos.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 Como no es posible que el ejército del cielo esté contado, o la arena del mar medida, así haré la simiente de mi siervo David y los levitas mis siervos.
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 Y vino la palabra del Señor a Jeremías, diciendo:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 ¿Has tomado nota de lo que estas personas han dicho, las dos familias, que el Señor escogió para sí mismo, los ha desechado? Esto lo dicen, mirando a mi gente con desprecio, en sus ojos, ya no es una nación.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 El Señor ha dicho: Si no he hecho el día y la noche, y si los límites del cielo y la tierra no han sido fijados por mí,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 Entonces, dejaré de cuidar de la simiente de Jacob y de David mi siervo, de modo que no tomaré de su descendencia para ser gobernantes sobre la simiente de Abraham, Isaac y Jacob; porque haré volver su cautividad y tendré misericordia de ellos.
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”

< Jeremías 33 >