< Isaías 34 >

1 Acércate, naciones, y oye; Toma nota, pueblos, que la tierra y todo lo que hay en ella oiga; El mundo y todos los que viven en él.
Ku zo kusa, ku al’ummai, ku kuwa saurara ku kasa kunne, ku mutane! Bari duniya ta ji, da kuma dukan abin da yake cikinta, duniya, da dukan abin da yake fitowa daga gare ta!
2 Porque el SEÑOR está enojado con todas las naciones, y su ira está ardiendo contra todos sus ejércitos. Él las ha destruido por completo, las ha entregado a la matanza al.
Ubangiji yana fushi da dukan al’ummai; hasalarsa tana a kan mayaƙansu. Zai hallaka su tas, zai ba da su a karkashe.
3 Sus cuerpos muertos serán gruesos sobre la faz de la tierra, y su olor subirá, y las montañas fluirán con su sangre, y todas las colinas se convertirán en nada.
Za a jefar da waɗanda aka kashe gawawwakinsu za su yi wari; duwatsu za su jiƙu da jininsu.
4 Y los cielos se enrollarán como el rollo de un libro: y todo ejército del cielo caerán, como una hoja muerta de la vid, o un fruto seco de la higuera.
Za a tumɓuke dukan taurarin sammai za a kuma nannaɗe sararin sama kamar littafi; dukan rundunar sama za su fāffāɗi kamar ganyayen da suka yanƙwane daga kuringa, kamar’ya’yan ɓauren da suka bushe daga itacen ɓaure.
5 Porque mi espada en el cielo está llena de ira; mira, está cayendo sobre Edom, para castigar a la gente, objeto de mi maldición.
Takobina ya sha zararsa a cikin sammai; duba, ya sauko cikin hukunci a kan Edom, mutanen da zan hallaka tas.
6 La espada del Señor está llena de sangre, está llena de sebo, de la sangre de los corderos y las cabras, con él sebo de los riñones del carnero: porque el Señor tiene un sacrificio en Bozra, y habrá una gran matanza en la tierra de Edom.
Takobin Ubangiji ya jiƙu da jini, ya rufu da kitse, jinin raguna da na awaki, kitse daga ƙodar raguna. Gama Ubangiji ya yi hadayar Bozra da kuma babban kisa a Edom.
7 Y los bueyes fuertes morirán junto con el ganado más pequeño. Y la tierra se empapará de sangre y el polvo se llenará de grasa y se hará ceniza.
Babban bijimin jeji zai fāɗi tare da su, maruƙan bijimi da manyan bijimai. Ƙasarsu za tă cika da jini, ƙura kuma zai cika da kitse.
8 Porque es el día del castigo del Señor, cuando él da pago por los males cometidos a Sión.
Gama Ubangiji yana da ranar ɗaukar fansa, shekarar ramuwa, don biya wa Sihiyona bukata.
9 Y sus arroyos se convertirán en aceite hirviendo, y su polvo en piedra ardiente, y toda la tierra se incendiará.
Za a mai da rafuffukan Edom rami, ƙurarta za tă zama kibiritun farar wuta; ƙasarta za tă zama rami mai ƙuna!
10 No se apagará de día ni de noche; su humo subirá para siempre; será un desperdicio de generación en generación; Nadie pasará jamás por ella.
Ba za a kashe ta ba dare da rana; hayaƙinta za tă yi ta tashi har abada. Daga tsara zuwa tsara za tă zama kango; babu wani da zai ƙara wucewa ta wurin.
11 Pero las aves del desierto tendrán su lugar allí; Será una herencia para el búho el cuervo: y se extenderá sobre ella el cordel de destrucción y la plomada de desolación.
Mujiyar hamada da mujiya mai kuka za su mallake ta; babban mujiya da hankaka za su yi sheƙa a can. Allah zai miƙe a kan Edom magwajin bala’i da ma’aunin kango.
12 Llamarán a los nobles y sus grandes desaparecerán y dirán: allí ya no hay reino, y todos sus jefes habrán llegado a su fin.
Sarakunanta ba za su kasance da wani abin da ake kira masarauta ba, dukan sarakunanta za su ɓace.
13 Y aparecerán espinas y ortigas en sus palacios, y espinos en sus fuertes torres; y los zorros harán sus agujeros allí, y será un lugar de reunión para avestruces.
Ƙayayuwa za su mamaye fadodinta ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya za su cika kagaranta. Za tă zama mazaunin diloli da gida don mujiyoyi.
14 Y las bestias de los lugares desolados se juntarán con los chacales, y los machos cabríos se clamarán unos a otros, incluso la lechuza nocturna vendrá y hará su descanso allí.
Halittun hamada za su sadu da kuraye, awakin jeji za su yi ta kiran juna; a can halittun dare su ma za su huta su kuma nemi wurin hutu wa kansu.
15 Allí hará su nido el búho real y pondrá sus huevos allí, y juntará a su cría bajo su sombra; allí los buitres se unirán cada macho con su hembra.
Mujiya za tă yi sheƙa a can ta zuba ƙwai; za tă ƙyanƙyashe su, ta kuma kula da’ya’yanta a inuwar fikafikanta; a can kuma shirwa za su taru, kowa da abokinsa.
16 Mira lo que está registrado en el libro del Señor: todos estos estarán allí, ninguno carecerá de su compañera; la boca del Señor ha dado la orden, y su espíritu los ha hecho venir juntos.
Duba a cikin littafin Ubangiji ka kuma karanta. Babu wani a cikin waɗannan da ya ɓace, babu ko ɗaya da ba ta da abokiya. Gama bakinsa ne ya ba da umarni, Ruhunsa kuma zai tara su wuri ɗaya.
17 Y ha echado la suerte, y por su mano ha medido con el cordel la tierra; será de ellos para siempre, su lugar de descanso de generación en generación.
Ya ba su rabonsu; hannunsa ya rarraba musu ta wurin awo. Za su mallake ta har abada su kuma zauna a can daga tsara zuwa tsara.

< Isaías 34 >