< Isaías 18 >

1 ¡Ay! Tierra del sonido de las alas, que está al otro lado de los ríos de Etiopía,
Kaiton ƙasar da ake jin ƙarar fikafikai a bakin kogunan Kush,
2 Que envía a sus representantes por el mar, incluso en barcos de papiro en las aguas. Regresa rápidamente, oh representantes, a una nación alta y suave, a un pueblo que causa temor a lo largo de toda su historia; una nación fuerte y opresora, cuya tierra está atravesada por ríos.
wadda ta aiko da jakadu ta teku cikin jiragen ruwan da aka yi da kyauro a bisa ruwa. Ku tafi, ku’yan saƙo masu sauri, zuwa ga dogayen mutane masu sulɓin jiki, zuwa ga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko tana jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba.
3 Todos ustedes pueblos del mundo, y ustedes que viven en la tierra, cuando una bandera se alza en las montañas, presten atención; y cuando suene la bocina, escuchen.
Ku dukan mutanen duniya, ku da kuke zama a duniya, sa’ad da aka ɗaga tutar a kan duwatsu, za ku gan shi, sa’ad da kuma aka busa ƙaho, za ku ji shi.
4 Porque esto es lo que el Señor me ha dicho: Estaré callado, observando desde mi lugar; como el calor claro cuando brilla el sol, como una niebla de rocío en el calor del verano.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Zan yi shiru in kuma duba a hankali daga mazaunina, kamar ƙuna mai zafi a hasken rana, kamar girgijen raba a lokacin girbi.”
5 Porque antes del momento de entrar en las uvas, después de la apertura del capullo, cuando la flor se haya convertido en una uva lista para triturar, quitará las pequeñas ramas con cuchillos, cortando, podando y tirara las ramas.
Gama kafin girbi, sa’ad da furanni suka karkaɗe furanni kuma suka zama’ya’yan inabin da suka nuna, zai faffalle rassan kuringar inabi da wuƙa, ya yanke ya kuma kwashe rassan da suka bazu.
6 Serán para las aves de las montañas, y para las bestias de la tierra: las aves de rapiña pasarán allí el verano, y las bestias salvajes de la tierra pasarán el invierno allí.
Duk za a bar su wa tsuntsayen dutse su ci da kuma namun jeji; tsuntsaye kuma za su ci rani a kansu, namun jeji kuma za su yi damina a kansu.
7 En ese tiempo se hará una ofrenda al Señor de ejércitos de un pueblo alto y suave, causando temor a través de toda su historia; una nación fuerte y opresora, cuya tierra está atravesada por ríos, una ofrenda llevada al lugar del nombre del Señor de los ejércitos, al Monte Sión.
A wannan lokaci za a kawo kyautai wa Ubangiji Maɗaukaki daga dogayen mutane masu sulɓin jiki, daga mutanen da ake jin tsoro a ko’ina, al’umma mai ƙarfin iko na jawabin da ba a saba ji ba, mai ƙasar da koguna suka raba. Za a kawo kyautai zuwa Dutsen Sihiyona, wurin da Sunan Ubangiji Maɗaukaki yake.

< Isaías 18 >