< Isaías 14 >
1 Porque el Señor tendrá misericordia de Jacob, y volverá a hacer de Israel su pueblo especial, y los pondrá en su tierra; y el hombre extranjero se juntara a ellos y se unirá a la familia de Jacob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Y el pueblo los llevará con ellos a su lugar, y los hijos de Israel les darán una herencia en la tierra del Señor como sirvientes y sirvientas, haciéndolos prisioneros de los cuales eran prisioneros; y serán gobernantes de sus amos.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Y será en el día en que el Señor te dé descanso de tu dolor, de tu angustia y del duro yugo que te habían puesto.
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 Que recitarás esta amarga canción contra el rey de Babilonia, y dirás: ¡Cómo ha terminado el cruel tirano! Como cesó la ciudad de oro;
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 La vara de los que hacen el mal, la vara de los gobernantes, es quebrantada por el Señor;
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 Aquel cuya vara estaba sobre los pueblos con una ira interminable, gobernando a las naciones con ira, con un gobierno incontrolado.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Toda la tierra está en reposo y está en silencio y estalla en cantos de alegría.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Incluso los árboles del bosque se alegran sobre ti, los árboles del Líbano, diciendo: Desde el momento de tu caída, ningún cortador de madera ha subido contra nosotros con un hacha.
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 El inframundo se conmueve con tu venida, los muertos están despiertos ante ti, incluso los fuertes de la tierra. Todos los reyes del mundo se han levantado de sus asientos. (Sheol )
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol )
10 Todos te responden y te dicen: ¿Te has vuelto débil como nosotros? ¿Has sido hecho como nosotros?
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Tu orgullo ha descendido al inframundo y el ruido de tus instrumentos de música; Los gusanos están debajo de ti, y tu cuerpo está cubierto con ellos. (Sheol )
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol )
12 ¡Qué grande es tu caída del cielo, oh lucero de la aurora, hijo de la mañana! ¿Cómo has caído a la tierra, tú que debilitabas a las naciones?
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Porque dijiste en tu corazón: Subiré al cielo, haré mi asiento más alto que las estrellas de Dios; Tomaré mi lugar en la montaña del lugar de reunión de los dioses, en las partes más alejadas del norte.
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 Subiré más alto que las nubes; Seré como el Altísimo.
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Pero descenderás al inframundo, incluso a sus partes más profundas. (Sheol )
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol )
16 Los que te vean te estarán observando con cuidado, pensarán profundamente y dirán: ¿Es éste el perturbador de la tierra, el agitador de los reinos?
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 Que hizo del mundo un desperdicio, derribando sus ciudades; Quien no dejó escapar a sus prisioneros de la cárcel.
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Todos los reyes de la tierra descansan en gloria, cada uno en su sepulcro.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 Pero tú, como un nacimiento antes de su tiempo, estás tendido sin lugar de descanso en la tierra; vestido con los cuerpos de los muertos que han sido arrojados a la espada, que descienden a las partes más bajas del inframundo; Un cuerpo muerto, aplastado bajo el pie.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 En cuanto a tus padres, no estarás unido a ellos en su lugar de descanso, porque has sido la causa de la destrucción de tu tierra y de la muerte de tu pueblo; la semilla del malvado no tendrá lugar en la memoria del hombre.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Prepara un lugar de muerte para sus hijos, por el mal hecho de sus padres; para que no puedan subir y tomar la tierra por su herencia, cubriendo la faz del mundo con ciudades.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 Porque subiré contra ellos, dice el Señor de los ejércitos, cortando el nombre y la descendencia de Babilonia, el hijo y el hijo del hijo, dice el Señor.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 Y te haré una herencia para el erizo y los estanques de agua; y la barreré con la escoba de la destrucción, dice el Señor de los ejércitos.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 El Señor de los Ejércitos ha hecho un juramento, diciendo: Lo que había pensado ciertamente se cumplirá, y lo que había planeado se llevará a cabo.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Para que el asirio sea quebrantado en mi tierra, y aplastado bajo mis montañas: allí será quitado su yugo, y su gobierno sobre ellos llegará a su fin.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Este es el propósito para toda la tierra, y esta es la mano extendida sobre todas las naciones.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Porque es el propósito del Señor de los ejércitos, y ¿quién lo hará inútil? cuando su mano está extendida, ¿por quién puede ser devuelta?
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 En el año de la muerte del rey Acaz, esta palabra llegó al profeta:
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 No se alegren, oh Filistea, todos ustedes, porque se quebró la vara que los oprimía; porque de la raíz de la serpiente saldrá una serpiente venenosa, y su fruto será una serpiente venenosa alada.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Y los más pobres de la tierra tendrán comida, y los necesitados tendrán un lugar de descanso seguro, pero tu simiente llegará a su fin por la necesidad de comida, y el resto de ustedes serán puestos a la espada.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 ¡Envía un clamor, oh puerta! ¡Gime de tristeza, pueblo! Desanímate, tu tierra ha quedado en nada, oh Filistea; porque sale un humo del norte, y todos mantienen su lugar en la fila.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 ¿Qué respuesta dará, entonces, mi pueblo a los representantes de la nación? Que el Señor es el constructor de Sión, y ella será un lugar seguro para los pobres de su pueblo.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”