< 2 Samuel 6 >

1 Y juntó David a todos los escogidos de Israel que eran treinta mil;
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 Y David, y todas las personas que estaban con él, fueron a Baala de Judá para obtener el cofre del pacto de Dios, sobre la cual se nombra el santo nombre, el nombre del Señor de los ejércitos, él cual mora entre los querubines.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 Y pusieron el arca de Dios en un carro nuevo y lo sacaron de la casa de Abinadab que estaba en la colina. Y Uza y Ahío, los hijos de Abinadab, eran los conductores del carro.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 Y Uza fue al lado del arca, mientras que Ahío iba delante de él.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 Y David y todos los hombres de Israel hicieron melodía ante el Señor con todo su poder, con cantos y con instrumentos de cuerda de bronce.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Y cuando llegaron al piso de grano de Nacón, Uza puso su mano en el arca de Dios para mantenerla a salvo en su lugar, porque los bueyes estaban fuera de control.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 Y la ira del Señor, que ardía contra Uza, envió destrucción sobre él porque había puesto su mano sobre el cofre del pacto de Dios, y allí llegó la muerte por el cofre del pacto de Dios.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 Y se enojó David por el arrebato de ira del Señor contra Uza, y le dio a ese lugar el nombre de Perez-uza, que es su nombre hasta hoy.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 Y tal fue el temor de David al Señor ese día, que dijo: ¿Cómo puedo dejar que el arca de Dios venga a mí?
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 Entonces, David no dejó que el arca del Señor volviera a él a la ciudad de David; sino que la apartaron y la pusieron en la casa de Obed-edom, de Gat.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 Y el cofre del Pacto del Señor estuvo en la casa de Obed-edom de Gat por tres meses, y el Señor envió una bendición sobre Obed-edom y toda su familia.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 Y dijeron al rey David: La bendición del Señor está sobre la familia de Obed Edom y sobre todo lo que tiene, por el arca de Dios. Y David fue y tomó el arca de Dios de la casa de Obed-edom al pueblo de David con alegría.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 Y cuando los que levantaban el arca del Señor habían dado seis pasos, hizo una ofrenda de un buey y una bestia gorda.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 Y David, vestido con un efod de lino, bailaba delante del Señor con todas sus fuerzas.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 Entonces David y todos los hombres de Israel tomaron el arca del Señor con clamores de alegría y sonando cuernos.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 Y cuando el cofre del pacto del Señor entró en la ciudad de David, Mical, la hija de Saúl, mirando por la ventana, vio al rey David bailando y saltando ante el Señor; y en su opinión él parecía tonto.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 Entonces tomaron el cofre del pacto del Señor y la pusieron en su lugar dentro de la tienda campaña que David la había levantado; y David hizo ofrendas quemadas y ofrendas de paz al Señor.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 Y después de que David hiciera las ofrendas quemadas y las ofrendas de paz, dio a la gente una bendición en nombre del Señor de los ejércitos.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 Y él dio a cada hombre y mujer entre todas las personas, entre todas las masas de Israel, un pastel de pan y una medida de vino y un pastel de uvas secas. Entonces todo el pueblo se fue, cada hombre a su casa.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 Entonces David volvió para dar una bendición a su familia. Y Mical, la hija de Saúl, se acercó a él y le dijo: ¡Cuán lleno de gloria estaba hoy el rey de Israel, que se dejó ver descubierto por sus sirvientas como una persona tonta que se descubre a sí misma sin vergüenza!
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 Y David dijo a Mical: Estaba bailando delante del Señor, que me puso sobre tu padre y sobre todos sus hijos, para hacerme gobernante sobre la gente del Señor, sobre su pueblo Israel.
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 Y me haré aún más vil que está vez, y me haré sentir aún más bajo: pero las sirvientas de las que hablabas me honrarán.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Y Mical, la hija de Saúl, no tuvo hijos hasta el día de su muerte.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >