< 2 Samuel 4 >

1 Y cuando el hijo de Saúl, Is-boset, tuvo noticias de que Abner había muerto en Hebrón, sus manos se debilitaron, y todos los israelitas se turbaron.
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 Y el hijo de Saúl tenía dos hombres, capitanes de bandas, uno llamado Baana y el otro Recab, hijos de Rimmon el Beerot, de la tribu de Benjamín; En un momento dado, Beerot fue tomado para ser parte de Benjamín.
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 Pero la gente de Beerot había ido en vuelo a Gitaim, donde han estado viviendo hasta el día de hoy.
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 Ahora Jonatán, hijo de Saúl, tuvo un hijo cuyos pies fueron dañados. Tenía cinco años cuando llegaron las noticias de la muerte de Saúl y Jonatán de Jezreel, y la mujer que lo cuidó lo levantó y cuando huyeron, y mientras ella lo estaba alejando tan rápido, se le cayó y sus pies fueron dañados. Su nombre era Mefiboset.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 Salieron Recab y Baana, los hijos de Rimón de Beerot, y llegaron a la casa de Is-boset en el calor del día, cuando él estaba descansando a la mitad del día. Ahora la mujer que guardaba la puerta estaba limpiando el grano, y el sueño la venció.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 Y Recab y su hermano Baana entraron sin ser vistos.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 Y cuando entraron en la casa, Is-boset estaba acostado en su cama en su dormitorio; Lo atacaron y lo mataron. Luego, cortándole la cabeza, se lo llevaron con ellos y pasaron por el camino a través del Arabá toda la noche.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 Entonces tomaron la cabeza de Is-boset a David en Hebrón, y dijeron al rey: Aquí está la cabeza de Is-boset, el hijo de Saúl, tu enemigo, que te habría quitado la vida; El Señor ha pagado el pago de los males de mi señor el rey Saúl y su simiente hoy.
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 Entonces David respondió a Recab y a su hermano Baana, los hijos de Rimón de Beerot, y les dijo: Por el Señor vivo, que me ha mantenido a salvo de todos mis problemas,
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 Cuando uno se acercó a mí con la noticia de la muerte de Saúl, creyendo que sería una buena noticia, lo tomé y lo maté en Siclag, que fue la recompensa que le di por su noticia.
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 ¿Cuánto más, cuando los hombres malvados hayan dado muerte a una persona recta, en su casa, durmiendo en su cama, recibiré de ustedes el pago de su sangre y voy a borrarlos de la tierra?
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 Y David dio órdenes a sus oficiales y los mataron, les cortaron las manos y los pies y los colgaron al lado del estanque en Hebrón. Pero tomaron la cabeza de Is-boset y la enterraron en él sepulcro de Abner en Hebrón.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >