< 2 Corintios 1 >

1 Pablo, Apóstol de Jesucristo por la voluntad de Dios, y Timoteo nuestro hermano, a la iglesia de Dios que está en Corinto, con todos los santos que están en toda Acaya:
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya.
2 Gracia y paz sea a ustedes de parte de Dios nuestro Padre y el Señor Jesucristo.
Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
3 Alabado sea el Dios y Padre de nuestro Señor Jesucristo, el Padre de las misericordias y el Dios de todo consuelo;
Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya.
4 Quien nos da consuelo en todos nuestros problemas, para que podamos consolar a otros que están en problemas, a través del consuelo que Dios nos consuela.
Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.
5 Porque a medida que sufrimos más del dolor que Cristo sufrió, a través de Cristo nuestro consuelo se hace más grande.
Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu.
6 Pero si somos afligidos, es para su consuelo y salvación; o si nos consuela, es para que ustedes también tengan consuelo y salvación y puedan soportar con fortaleza los mismos sufrimientos que también nosotros experimentamos.
Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha.
7 Y nuestra esperanza por ustedes es firme; sabiendo que al ser copartícipes de los sufrimientos, también lo serán en la consolación que viene de Dios.
Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.
8 Porque es nuestro deseo, hermanos, que no ignoren las tribulaciones que tuvimos en Asia, fue una prueba tan grande, que ya no podíamos resistir más, hasta perdimos la esperanza de salir con vida:
Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu.
9 nos sentíamos como sentenciados a muerte, él propósito de esto, para no poner nuestra esperanza en nosotros mismos, sino en Dios que puede dar vida a los muertos:
Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu.
10 Quien nos libró y de una muerte tan grande y nos librará, y en quién hemos puesto nuestra esperanza que nos seguirá librando;
Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.
11 Ustedes, al mismo tiempo, colaborando con su oración por nosotros; si muchos oran por nosotros, la alabanza de agradecimiento por muchas personas de nuestra parte darán a Dios por todas las bendiciones concedidas a favor nuestro.
Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.
12 Porque nuestra gloria es está: el testimonio de nuestra conciencia, que en sencillez y sinceridad santa, nos hemos conducido en el mundo y sobre todo en relación con ustedes; no en la sabiduría de la carne, sino en la gracia de Dios nos ha ayudado a vivir así.
Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah.
13 Porque en nuestras cartas no les escribimos cosas distintas de lo que puedan leer o entender, espero que lleguen a entender perfectamente hasta el final:
Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya,
14 Como ya lo han entendido en parte, para decir que somos su gloria; la razón de su gozo, de la misma manera que son nuestra gloria en el día del Señor Jesús.
kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.
15 Con esta confianza, ya había pensado venir a ustedes antes, para que puedan tener una doble bendición espiritual;
Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu.
16 pensaba visitarlos primeramente al pasar camino a Macedonia, y después, al regresar, visitarlos otra vez; así ustedes podrían ayudarme a seguir mi viaje a Judea.
Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.
17 Si entonces tenía ese propósito, ¿parecía estar cambiando de repente? ¿o soy guiado en mis propósitos por la carne, diciendo: sí, hoy y no, de acuerdo a impulsos humanos?
Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce “I, i” da “A, a, a, a” a lokaci guda?
18 Dios es testigo, nuestra palabra para ustedes no es Sí y No al mismo tiempo.
Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin ''I'' da ''A'a'' a lokaci guda.
19 Porque el Hijo de Dios, Jesucristo, a quien estábamos predicando entre ustedes, yo y Silvano y Timoteo, no era Sí y No, sino que ha sido Si en él;
Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba “I” da “A, a” ba ne. Maimakon haka, Shi “I” ne a kodayaushe.
20 Porque todas las promesas de Dios son Sí, y en Jesucristo Amén, para la gloria de Dios por medio de nosotros.
Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa ''Amin'' zuwa ga daukakar Allah.
21 Y el que hace fuerte nuestra fe juntamente con ustedes en Cristo, y nos ha dado de su unción, es Dios;
Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu.
22 Y es él quien nos ha sellado, y nos dio el Espíritu, como garantía en nuestros corazones de lo que vamos a recibir, la gloria venidera.
Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.
23 Pero Dios es mi testigo de que fue una pena para ustedes que no haya venido a Corinto en ese momento.
Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne.
24 No es que tengamos autoridad sobre su fe, sino que queremos colaborar con ustedes, para que se gocen; porque por la fe están firmes.
Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.

< 2 Corintios 1 >